Aminiya:
2025-07-11@00:22:10 GMT

Ana zargin wani mutum da kashe ɗan maƙwabtansa a Sakkwato

Published: 25th, May 2025 GMT

An shiga ruɗani a unguwar CBN Quarters da ke cikin birnin Sakkwato, inda wani ƙaramin yaro ɗan shekara huɗu mai suna Ayman Abubakar, ya ɓace, amma daga bisani aka gano gawarsa a cikin ramin sokawe.

Ana zargin wani maƙwabcin iyayen yaron da wata mata da aikata wannan ɗanyen aiki.

An kashe matashi yayin rikici a ƙauyukan Kano Gwamnatin Gombe za ta taimaki ’yar shekara 14 da aka yi wa auren dole

Ƙngiyoyi da ke fafutukar kare haƙƙin yara da martabar bil adama sun bayyana wannan kisa a matsayin babban cin zarafi.

A cikin wata sanarwar haɗin gwiwa da suka fitar, shugaban NACTAL na ƙasa Abdulganiyu Abubakar, Usman Ahmad daga ƙungiyar kare haƙƙin yara, da Rabi’u Bello Gandi shugaban hukumar kare cin zarafin jinsi, sun yi Allah-wadai da kisan yaron.

“Kashe wannan ƙaramin yaro cin zarafi ne na keta haƙƙin ɗan Adam, kuma lamarin da ya saɓa da doka.

“Wannan mummunan abu ne da ke ƙara nuna irin haɗuran da yara ke fuskanta a cikin al’umma.”

Ƙungiyoyin sun buƙaci a gudanar da bincike don gano gaskiya tare da ɗaukar matakin hukunta duk wanda ke da hannu a kisan.

“Muna kira da a tabbatar da an yi gaskiya da adalci, a kuma hukunta waɗanda ke da hannu a kisan Ayman. Hakazalika, ya zama dole a riƙa bayyana wa jama’a irin ci gaban da ake samu a yayin bincike lokaci bayan lokaci.”

Sun jaddada buƙatar a ɗauki matakan gaggawa na kare yara daga faɗa wa hannun miyagu.

“Kare haƙƙin yaron ɗan Najeriya lamari ne da ya kamata a bai wa fifiko a ƙasa, a daina wasa da shi.”

Mahaifin Ayman, Dakta Abubakar, ya bayyana damuwarsa kan yadda lamarin ya faru.

“Na rasa ɗana ne ranar 29 ga watan Maris, bayan ya dawo daga sallar La’asar. Mun yi ta nemansa har tsawon sati bakwai ba tare da nasara ba. Daga baya sai aka gano gawarsa a cikin ramin sokawe.”

Ya roƙi al’umma su mara masa baya wajen ganin an yi wa ɗansa adalci.

Rundunar ’yan sandan jihar, tabbatar da cewa ta kama waɗanda ake zargi, kuma an fara gudanar da bincike a kansu.

Ƙungiyoyin sun yi alƙawarin ganin cewa sun bibiyu lamarin don tabbatar da gaskiya da adalci.

“Za mu tsaya tare da iyayen Ayman domin tabbatar da cewa an yi adalci. Adalci ga Ayman, adalci ne ga kowa.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sakkwato Sokawe yaro zargi tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Gwagwarmayar Falasdinu Sun Halaka Sojojin Mamaya Biyar Tare Da Jikkata Wasu Goma Na Daban

Sojojin mamayar Isra’ila 5 ne suka halaka yayin da wasu 10 suka jikkata a wani gagarumin farmaki da aka kai musu a arewacin Gaza

Sojojin mamayar Isra’ila 5 ne suka sheka lahira sannan wasu akalla 10 suka jikkata a wani gagarumin farmaki da ‘yan gwagwarmaya suka kai a Beit Hanoun da ke arewacin zirin Gaza. Har yanzu wani sojan Isra’ila ya bace kamar yadda kafafen yada labaran haramtacciyar kasar Isra’ila suka ruwaito.

Cibiyar yada labaran Falasdinu ta watsa rahoton cewa, lamarin ya faru ne a lokacin da s’yan gwagwarmaya suka tayar da bam a cikin wata motar sojin Isra’ila mai sulke dauke da sojoji, sannan suka nufi wani mutum-mutumi da ke dauke da harsashi da makami mai linzami a lokacin da ake shirya shi.

Hare-haren dai sun auka ne kan dakarun ceto na Isra’ila da suka garzaya zuwa wurin, yayin da mazauna birnin Ashkelon suka ji karar fashewar wani babban bam, a cewar shafukan yanar gizo na Isra’ila, inda suka ce daya daga cikin wadanda suka jikkata wani babban jami’i ne.

Sojojin da aka kai wa harin na sashen injiniyan Yahalom ne, wanda ke da alhakin yin tarko da kuma tayar da bama-bamai a gidajen Falasdinawa a zirin Gaza, a cewar wakilin Al Jazeera na Falasdinu, Najwan Samri.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe mutum ɗaya da ƙona gidaje sama da 100 a Taraba
  • An gurfanar da wasu kan zargin kashe matafiya bikin aure a Jos
  • Kwamandan Sojin Iran Ya Jaddada Kare Kan Iyakokin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 22 Kan Zargin Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato
  • Isra’ila ta kashe Falasdinawa 24 a Zirin Gaza
  • Sojoji Sun Kai Hari Maɓoyar Boko Haram A Borno, Sun Kashe Wasu ‘Yan Ta’adda
  • Zagaye na 5 A Tattaunawar Gaza da HKI  Ya tashi ba tare da Sun Dai-daita ba A Doha
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 13 a ƙauyukan Neja
  • Ana zargin takalar faɗa tsakanin fadar Aminu Ado da Sanusi II
  • ‘Yan Gwagwarmayar Falasdinu Sun Halaka Sojojin Mamaya Biyar Tare Da Jikkata Wasu Goma Na Daban