Aminiya:
2025-07-24@23:31:34 GMT

Mutanen da suka mutu a ambaliyar Neja sun ƙaru zuwa 88 —NSEMA

Published: 30th, May 2025 GMT

Yawan mutanen da suka rasu a sakamakon mummunar ambaliyar ruwan sama a yankin Ƙaramar Hukumar Mokwa ta Jihar Neja ya ƙaru zuwa 88.

Shugaban Sashen Ayyuka na Hukumar ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), Husseini Isah, ne ya sanar da haka a ranar Juma’a.

Ya ce, “adadin mamatan na ci gaba da ƙaruwa, amma a halin yanzu mun ƙirga mutum 88.

” Hussain Ya ƙara da cewa ana ci gaba aikin ceto.

Aminiya ta ruwaito cewa wasu mutum 12 ’yan gida ɗaya suna cikin mutanen da ambaliyar ta yi ajalinsu.

NAJERIYA A YAU: Yaya Girman Matsalar Rashin Tsaro A Shekaru Biyun Tinubu? Faransa ta haramta shan sigari a cikin jama’a

Ambaliyar ta yi rusa da gidaje sama da 50 tare da sanye murare da dama.

Tun da farko kakakin Hukumar NSEMA, Ibrahim Audu Husseini, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa, “akwai yiwuwar yawan mutanen da suka mutu da sauran asarar da aka yi za su ƙaru, saboda akwai masu aikin ceto a wurare daban-daban.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliya

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: An ƙaddamar da aikin sabunta ginin Majalisar Dokokin Bauchi

Gwamna Bala Muhammad ya ƙaddamar da aikin gyare-gyare da sabunta ginin Majalisar Dokokin Bauchi kan kuɗin da ya haura Naira biliyan bakwai, wanda ya haɗa da inganta kayan aiki, ofisoshi, da kuma gina sabon ofishin hukumar kula da harkokin majalisa.

A yayin ƙaddamarwar da aka gudanar ranar Talata, Gwamna Bala ya bayyana cewa wannan gyara na cikin shirin gwamnatinsa na sauya fasalin birane da samar da muhalli mai kyau ga ma’aikata domin sauƙaƙa aikinsu.

Majalisar Dattawa ta sahale wa Tinubu karɓo rancen $21bn a ƙetare UNICEF na zargin Gwamnatin Nijeriya da cin zarafin ƙananan yara

Ya ƙara da cewa tuni aka riga aka biya rabin kuɗin aikin domin tabbatar da cewa aikin ya kammala a kan lokaci.

Kwamishinan gidaje da muhalli, Danlami Ahmed Kawule, ya ce aikin zai ƙunshi gyaran zauren majalisar, ofisoshin mambobi, gina sabbin hanyoyin ruwa da wutar lantarki na masu amfani da hasken rana, da kuma gyara titunan cikin majalisar.

Tun da farko, mambobin majalisar sun koma ofishin tsohon mataimakin gwamna domin ci gaba da aikinsu yayin da ake gudanar da gyaran.

Gwamnan ya yaba wa fahimtar da ke tsakaninsa da majalisar, yana mai cewa hakan ne ke bai wa gwamnati damar aiwatar da ayyukan ci gaba.

Kakakin Majalisar, Abubakar Y. Suleiman, ya bayyana godiya bisa wannan ci gaba, yana mai cewa haɗin kai tsakanin majalisar zartarwa da majalisar dokoki na taka muhimmiyar rawa wajen kawo ci gaba a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Iran Tana Cikin Kasashe Biyar Na Duniya Da Suka Ci Gaba Wajen Kiwon Dabbobi
  • Kwalara: Mutum 13 sun mutu sama da 236 na jinya a Neja
  • Ɓullar Kwalara: Mutum 13 sun mutu sama da 236 na jinya a Neja
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 95 a Neja, sun ceto mutum 138 da aka sace
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 11 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Sakkwato
  •  Fiye Da  Kungiyoyin 100 A Duniya Sun Yi Gargadi Akan Halin Yunwa Da HKi Ta Jefa Mutanen Gaza A Ciki
  • NEDC ta raba wa mutanen da ambaliya ta shafa kayan gini a Yobe
  • HOTUNA: An ƙaddamar da aikin sabunta ginin Majalisar Dokokin Bauchi
  • Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh
  • Magudnar Ruwa Ta Yi Ajalin Rayuka Hudu A Zangon Kaya, Kano