Aminiya:
2025-05-31@21:44:24 GMT

Mutanen da suka mutu a ambaliyar Neja sun ƙaru zuwa 88 —NSEMA

Published: 30th, May 2025 GMT

Yawan mutanen da suka rasu a sakamakon mummunar ambaliyar ruwan sama a yankin Ƙaramar Hukumar Mokwa ta Jihar Neja ya ƙaru zuwa 88.

Shugaban Sashen Ayyuka na Hukumar ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), Husseini Isah, ne ya sanar da haka a ranar Juma’a.

Ya ce, “adadin mamatan na ci gaba da ƙaruwa, amma a halin yanzu mun ƙirga mutum 88.

” Hussain Ya ƙara da cewa ana ci gaba aikin ceto.

Aminiya ta ruwaito cewa wasu mutum 12 ’yan gida ɗaya suna cikin mutanen da ambaliyar ta yi ajalinsu.

NAJERIYA A YAU: Yaya Girman Matsalar Rashin Tsaro A Shekaru Biyun Tinubu? Faransa ta haramta shan sigari a cikin jama’a

Ambaliyar ta yi rusa da gidaje sama da 50 tare da sanye murare da dama.

Tun da farko kakakin Hukumar NSEMA, Ibrahim Audu Husseini, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa, “akwai yiwuwar yawan mutanen da suka mutu da sauran asarar da aka yi za su ƙaru, saboda akwai masu aikin ceto a wurare daban-daban.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliya

এছাড়াও পড়ুন:

Yemen: Matukar Gaza Tana Fuskantar Yaki, To Babu Tsaro A HKI

Miliyoyin Mutanen Kasar Yemen sun yi gangamin a jihohi 14 na fadin kasar domin nuna goyon bayan Gaza.

A cikin birnin Sanaa an yi taron ne a dandalin Saba’in a yau juma’a da mahalartansa suka rika bayar da taken nuna kin amincewa da halin da mutanen Gaza suke ciki na yunuwar da aka jefa su da kuma ci gaba da yi musu kisan kiyashi.

Bugu da kari masu gangamin sun rika bayyana cewa; Taimakawa mutanen Gaza, kai wa manzon Allah cika-makin annabawa, manzon Allah ( s.a.w) dauki ne, kuma taimakon masallacin Kudus ne.

Haka nan kuma masu gangamin na birnin Sanaa sun yi tir da kutsa masallacin kudus da yahudawa ‘yan share wuri zauna su ka yi. Har ila yau, mutanen sun bayyana cewa; Fitowar da su ka yi, nau’in jihadi ne da kuma amsa umarnin Allah da yin jihadi a tafarkinsa da kuma neman yardarsa.

Baya ga birnin San’aa an kuma yi wasu gangamin a cikin birane 14 na fadin kasar ta Yemen.

Kasar Yemen dai tana ci gaba da kai wa manufofin HKI hare-hare saboda ci gaba da tafka laifukan yaki da take yi a Gaza, tare da jaddada cewa ba za su daina ba har idan an kawo karshen yakin na Gaza.

Sojojin Yemen ta bakin kakakinsu Janar Yahya Sari, sun sanar da kakaba takunkumi akan tasoshin jiragen sama da na ruwa na HKI. Daga lokaci zuwa lokaci sojojin na Yemen suna harba makamai masu linzami akan filin saukar jirgin sama na “Ben-Gorion” da kuma tashar jirgin ruwa ta “Haifa”.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Mutanen Da Suka Rasa Rayukansu A Ambaliyan Ruwa A Jihar Niger Na Najeriya Ya Kai 151
  • Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115
  • Mutanen da suka rasu a ambaliyar ruwa a Neja sun ƙaru zuwa 151
  • Mutanen da suka rasu a ambaliyyar ruwa a Neja sun ƙaru zuwa 151
  • Gwamnatin Tarayya Ta Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Ambaliyar Garin Mokwa A Neja
  • Yemen: Matukar Gaza Tana Fuskantar Yaki, To Babu Tsaro A HKI
  • Yadda ambaliyar Neja ta ci mutum 12 ’yan gida daya
  • NAHCON ta kammala jigilar maniyyata aikin hajjin 2025
  • Ambaliyar ruwa ta kashe sama da mutum 50 a Neja