NDLEA ta kama maniyyata aikin hajji ɗauke da hodar iblis
Published: 29th, May 2025 GMT
Shugaban Hukumar da ke yaƙi da shan miyagun kwayoyi ta Najeriya NDLEA Janar Buba Marwa (mai ritaya), a ranar Laraba, ya bayyana kamen wasu mutum biyu da suka yi yunƙurin safarar hodar Iblis a lokacin da ake jigilar maniyyata aikin hajji a kan hanyarsu ta zuwa ƙasar Saudiyya don gudanar da Hajjin bana.
Da yake jawabi a wajen buɗe taron kwamitin kula da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi a Abuja, Marwa ya bayyana cewa, waɗanda ake zargin sun haɗiyi miyagun ƙwayoyin ne, inda suka nuna cewa su Musulmi ne masu kishin addini da suke shirin gudanar da aikin hajji.
’Yan bindiga sun kashe makiyaya 2, sun sace shanu 320 a Kaduna Ɗalibai sun maƙale lokacin da gini ya rufta suna jarrabawa“Kwanaki kaɗan da suka wuce, mun kama wasu maniyyata biyu da za su je ƙasar Saudiyya aikin Hajji, inda suka haɗiye hodar iblis, suna nuna cewa za su je ƙasar ne don yin hajjin bana,” in ji shi.
Shugaban Hukumar ta NDLEA ya bayyana damuwarsa kan yadda rukuni masu aikata laifuka ke ta’ammali da miyagun ƙwayoyi a ƙasashen duniya musamman a lokacin aikin Hajji.
“Mun sha ganin faruwar hakan inda ake yaudarar mutane da sunan aikin Hajji.
Shekaru biyu da suka wuce, an damfari mata uku. Wasu mutane sun yi tayin biyan tikitin su, da biza da sauransu. Kafin su tafi an ba su wata ’yar ƙaramar jaka don kai wa wani da ake zaton ɗan uwa ne a ƙasar Saudiyya. Ba su san shi ba, an ɗinke hodar iblis ɗin a cikin jaka,” in ji shi.
Marwa ya lura cewa, duk da ƙalubalen kuɗaɗe da suka shafi cikakken aiwatar da babban tsarin hana shan muggan ƙwayoyi na ƙasa (2021-2025), hukumar ta ci gaba da jajircewa kan manufar ayyukanta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hukumar NDLEA Janar Buba Marwa
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun halaka mayakan ISWAP da dama a Borno
Dakarun sojojin Najeriya sun dakile wani harin hadin gwiwa da ‘yan ta’addar Boko Haram da ISWAP suka kai a yankin Marte da ke jihar Borno, inda suka kashe wasu da dama daga cikin maharan.
Majiyar leken asirin hedikwatar sojan Najeriya ta tabbatar da cewa harin ya faru ne da misalin karfe 1:35 na wayewar safiyar talata 27 ga watan Mayu.
Majiyar ta ce wasu ’yan ta’adda da ba a tabbatar da adadin su ba sun kai hari a bataliya ta 50 da ke Marte.
Kotu ta ci su El-Rufa’i tarar miliyan 900 Tinubu ya ɗaga darajar Kwalejin Kimiyya ta Kabo Zuwa Jami’ar Fasaha ta TarayyaDakarun da ke samun goyon bayan wata tawaga ta runduna ta 24 da bataliya ta musamman ta 134, sun yi gaggawar fafatawa da ’yan ta’addan a wani kazamin fadan da aka kwafsa.
A cewar rahoton, dakarun rundunar sojojin saman Najeriya na Operation Hadin Kai, ta aiwatar da aikin leken asiri ta sama, da kuma dauki ba dadi, wanda ya taka rawar gani wajen fatattakar ’yan tada kayar bayan da suka tsere.
Majiyar ta ce sojojin sun yi nasarar dakile harin tare da dawo da cikakken iko a yankin, yayin da ake ci gaba da gudanar da aikin zakulo abubuwan da suka rage da kuma kwato makamai da kayan aikin da ’yan ta’addan ke amfani da su.
“Sojoji biyu sun rasa ransu a yayin wannan farmaki, sannan an samu wasu asarorin kayayyakin da suka hada da lalacewar wata babbar mota mai dauke da bindiga da kuma tayar wata motar sojoji,” in ji majiyar.
Harin na baya-bayan nan a Marte na zuwa ne a daidai lokacin da sojoji ke dada kai hare-hare a yankin tafkin Chadi da arewacin Borno, inda kungiyoyin ISWAP da Boko Haram suka yi yunkurin sake kafa sansanoninsu.
A halin da ake ciki dai, ana ci gaba da sanya ido sosai kan harkokin tsaro a jihar Borno, inda ake ci gaba da gudanar da sintiri da tattara bayanan sirri da nufin hana kutse a nan gaba, in ji majiyar ta sojan Najeriya.