NDLEA ta kama maniyyata aikin hajji ɗauke da hodar iblis
Published: 29th, May 2025 GMT
Shugaban Hukumar da ke yaƙi da shan miyagun kwayoyi ta Najeriya NDLEA Janar Buba Marwa (mai ritaya), a ranar Laraba, ya bayyana kamen wasu mutum biyu da suka yi yunƙurin safarar hodar Iblis a lokacin da ake jigilar maniyyata aikin hajji a kan hanyarsu ta zuwa ƙasar Saudiyya don gudanar da Hajjin bana.
Da yake jawabi a wajen buɗe taron kwamitin kula da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi a Abuja, Marwa ya bayyana cewa, waɗanda ake zargin sun haɗiyi miyagun ƙwayoyin ne, inda suka nuna cewa su Musulmi ne masu kishin addini da suke shirin gudanar da aikin hajji.
’Yan bindiga sun kashe makiyaya 2, sun sace shanu 320 a Kaduna Ɗalibai sun maƙale lokacin da gini ya rufta suna jarrabawa“Kwanaki kaɗan da suka wuce, mun kama wasu maniyyata biyu da za su je ƙasar Saudiyya aikin Hajji, inda suka haɗiye hodar iblis, suna nuna cewa za su je ƙasar ne don yin hajjin bana,” in ji shi.
Shugaban Hukumar ta NDLEA ya bayyana damuwarsa kan yadda rukuni masu aikata laifuka ke ta’ammali da miyagun ƙwayoyi a ƙasashen duniya musamman a lokacin aikin Hajji.
“Mun sha ganin faruwar hakan inda ake yaudarar mutane da sunan aikin Hajji.
Shekaru biyu da suka wuce, an damfari mata uku. Wasu mutane sun yi tayin biyan tikitin su, da biza da sauransu. Kafin su tafi an ba su wata ’yar ƙaramar jaka don kai wa wani da ake zaton ɗan uwa ne a ƙasar Saudiyya. Ba su san shi ba, an ɗinke hodar iblis ɗin a cikin jaka,” in ji shi.
Marwa ya lura cewa, duk da ƙalubalen kuɗaɗe da suka shafi cikakken aiwatar da babban tsarin hana shan muggan ƙwayoyi na ƙasa (2021-2025), hukumar ta ci gaba da jajircewa kan manufar ayyukanta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hukumar NDLEA Janar Buba Marwa
এছাড়াও পড়ুন:
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka
Ficewar Amurka daga yarjejeniyoyin kasa da kasa da hukumomin duniya ba sabon labari ba ne, don haka mene ne abun mamaki idan ta bar UNESCO a karo na uku? Wani binciken jin ra’ayoyin jama’a da CGTN ta gudanar ya nuna cewa kashi 84.2 cikin dari na wadanda suka bayyana rayoyinsu ba su yi mamakin wannan matakin ba, lamarin da ke nuni da cewa, kasashen duniya sun saba da halayyar “kauracewar” Amurka. Wannan mataki na “Amurka ta zamanto farko” yana kara ingiza bukatar tsarin damawa da mabambantan bangarori na hakika cikin hanzari.
Hujjar gwamnatin Amurka a wannan karon ta kasance a sarari, watau ta zargi UNESCO da ci gaba da zurfafa tabbatar da “mabambantan tsarin zamantakewa da al’adu” wadanda suka ci karo da manufarta ta “Amurka ta zamanto farko”. A cewar sakamakon binciken, kashi 93.5 na masu bayyana raayoyi sun soki Amurka bisa mayar da cibiyoyin kasa da kasa a matsayin kayan aikin cimma muradunta na siyasa.
Binciken jin ra’ayoyin ya nuna cewa kashi 90.7 cikin dari na wadanda suka bayyana raayoyinsu suna kallon ficewar baya-bayan nan a matsayin karin tabbaci na yadda Amurka ke nuna son zuciya saboda Isra’ila, yayin da kashi 91.1 cikin dari na jamaar da suka bayyana raayoyin nasu suka nuna cewa, tsarin mu’amalarta da hukumomin kasa da kasa bai zamo mai alfanu ga wata babbar kasa ba, ko kuma biyan bukatun kasashen duniya.
Wanda aka gudanar a kafofin CGTN na harsunan Ingilishi, da Sifaniyanci, Faransanci, Larabci, da Rashanci, binciken ya tattaro raayoyin jamaa 9,097 cikin sa’o’i 24. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp