Aminiya:
2025-11-02@15:13:16 GMT

NDLEA ta kama maniyyata aikin hajji ɗauke da hodar iblis

Published: 29th, May 2025 GMT

Shugaban Hukumar da ke yaƙi da shan miyagun kwayoyi ta Najeriya NDLEA Janar Buba Marwa (mai ritaya), a ranar Laraba, ya bayyana kamen wasu mutum biyu da suka yi yunƙurin safarar hodar Iblis a lokacin da ake jigilar maniyyata aikin hajji a kan hanyarsu ta zuwa ƙasar Saudiyya don gudanar da Hajjin bana.

Da yake jawabi a wajen buɗe taron kwamitin kula da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi a Abuja, Marwa ya bayyana cewa, waɗanda ake zargin sun haɗiyi miyagun ƙwayoyin ne, inda suka nuna cewa su Musulmi ne masu kishin addini da suke shirin gudanar da aikin hajji.

’Yan bindiga sun kashe makiyaya 2, sun sace shanu 320 a Kaduna Ɗalibai sun maƙale lokacin da gini ya rufta suna jarrabawa

“Kwanaki kaɗan da suka wuce, mun kama wasu maniyyata biyu da za su je ƙasar Saudiyya aikin Hajji, inda suka haɗiye hodar iblis, suna nuna cewa za su je ƙasar ne don yin hajjin bana,” in ji shi.

Shugaban Hukumar ta NDLEA ya bayyana damuwarsa kan yadda rukuni masu aikata laifuka ke ta’ammali da miyagun ƙwayoyi a ƙasashen duniya musamman a lokacin aikin Hajji.

“Mun sha ganin faruwar hakan inda ake yaudarar mutane da sunan aikin Hajji.

Shekaru biyu da suka wuce, an damfari mata uku. Wasu mutane sun yi tayin biyan tikitin su, da biza da sauransu. Kafin su tafi an ba su wata ’yar ƙaramar jaka don kai wa wani da ake zaton ɗan uwa ne a ƙasar Saudiyya. Ba su san shi ba, an ɗinke hodar iblis ɗin a cikin jaka,” in ji shi.

Marwa ya lura cewa, duk da ƙalubalen kuɗaɗe da suka shafi cikakken aiwatar da babban tsarin hana shan muggan ƙwayoyi na ƙasa (2021-2025), hukumar ta ci gaba da jajircewa kan manufar ayyukanta.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hukumar NDLEA Janar Buba Marwa

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025 Manyan Labarai NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa October 31, 2025 Labarai Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia Suluhu Hassan ta yi tazarce
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC