A ganin kasar Sin, kafuwar hukumar za ta ba da damar kara shigar da kasashe masu tasowa cikin aikin kula da al’amuran duniya, da tabbatar da daidaita rikici ta wata hanya mai adalci, da bai wa kasashe masu tasowa karin ikon fadin albarkacin bakinsu.

 

A shekarun baya, kasar Sin ta taimaka wajen tabbatar da samun sulhu tsakanin kasar Saudiyya da ta Iran, da ganin yadda bangarorin siyasa daban daban na Falasdinawa suka kulla yarjejeniyar sulhu a birnin Beijing na Sin.

Kana a wannan karo, kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa a kokarin kulla yarjejeniyar kafa hukumar shiga tsakani. Duk wadannan abubuwa sun nuna yadda Sinawa suke darajanta sulhu da zaman lumana a duniya. (Bello Wang)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Matsayin Iran Na Rashin Tunanin Kera Makamin Nukiliya

Shugaban kasar Iran ya jaddada cewa: Makaman nukiliya ba su da gurbi a cikin akidar Jamhuriyar Musulunci ta Iran

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya jaddada cewa: Iran ba za ta taba yin watsi da haƙƙin da doka ta tanada ba ta fannin inganta sinadarin uranium, domin inganta harkar kiwon lafiya, aikin gona da masana’antu, yana mai jaddada cewa: makaman nukiliya ba su da gurbi a cikin koyarwar Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

A yayin ziyarar da ya kai masarautar Oman, shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian, a wata hira da gidan talabijin na kasar, ya yi bayani kan batutuwan da suka shafi kasashen biyu, da kuma muradun yankin da na kasa da kasa na Iran da Oman, da kuma muhimman batutuwan da suke faruwa a duniya.

Ya kamata a lura da cewa: Wannan ziyara ta zo ne a cikin tsarin karfafa zumunci da fitacciyar alakar da ke tsakanin masarautar Oman da Jamhuriyar Musulunci ta Iran, da goyon bayan bangarori daban-daban na hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu, da kuma cikin tsarin muradun da shugabannin kasashen biyu ke da shi na kara karfafa da raya wannan dangantaka. An tattauna fannoni daban-daban na hadin gwiwa da suka yi daidai da muradun kasashen abokan juna da kuma biyan bukatunsu, musamman ma a fannin ci gaban yankin da kasa da kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Tattauna Darakta-Janar Na Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Gargadi Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Da Wasu Kasashe
  • An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya
  • Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed
  • Iran Ta Kaddamarda Sabbin Magunguna Har 23 Tare Riga Kafin HPV A Karon Farko A Kasar
  • Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa
  • An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Matsayin Iran Na Rashin Tunanin Kera Makamin Nukiliya