NAJERIYA A YAU: Tasirin Dangantakar Bangaren Zartarwa Da Na Majalisa A Kan Talaka
Published: 26th, May 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
A tsarin mulkin dimokuraɗiyya, dangantaka tsakanin bangaren zartarwa da majalisun dokoki tana taka muhimmiyar rawa wajen gudanar da shugabanci a tsakanin al’umma.
A galibin kasashe masu bin tsarin na dimokuraɗiyya, ’yan majalisa kan kasance masu wakiltar al’umma da kare muradunta, da sa ido da kuma bayar da shawarwarin da suka dace ga bangaren zartarwa domin ci-gaban kasa.
Sai dai a Najeriya, a wasu lokutan akan zargi ’yan majalisa da zama ’yan-amshin-Shata.
Ko me ya sa haka? Shin yaya ya kamata dangantaka ta kasance a tsakanin bangaren zartarwa da majalisar dokoki a tsarin mulkin dimokuraɗiyya?
NAJERIYA A YAU: Dalilin ’Yan Adawa Na Ƙulla Ƙawance A Ƙarƙashin Inuwar ADC DAGA LARABA: “Abba Al-Mustafa Ba Shi Da Hurumin Dakatar Da Fina-finanmu”Wannan shi ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai duba.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Majalisar Dokoki Majalisar Zartarwa
এছাড়াও পড়ুন:
Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Ce: Dole Ne A Dauki Kwararan Matakan Don Dakatar Da Laifukan Gaza
Jagoran juyin juya halin Musulunci ya jaddada cewa: Dole ne a dauki kwararan matakai don dakatar da laifukan da ake yi a Gaza
A yayin ganawarsa da fira ministan Pakistan Shehbaz Sharif da tawagarsa a yammacin yau, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada wajabcin gudanar da ayyukan hadin gwiwa da inganci tsakanin kasashen Iran da Pakistan domin dakile laifukan da yahudawan sahayoniyya suke aikatawa a Gaza.
A farkon taron, Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana matsayin Pakistan na musamman a duniyar Musulunci, inda ya bayyana jin dadinsa da kawo karshen yakin da ake yi tsakanin Pakistan da Indiya, tare da bayyana fatansa na warware sabanin da ke tsakanin kasashen biyu ta hanyar lumana.
Haka nan kuma ya yi ishara da matsayar da Pakistan ta dauka kan batun Falastinu a cikin wadannan shekaru da suka gabata, yana mai cewa: Duk da cewa a cikin ‘yan shekarun nan a kodayaushe ana fuskantar kalubale ga kasashen musulmi na kulla alaka da yahudawan sahayoniyya, Pakistan ba ta taba samun irin wadannan fitintinu ba.