More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A tsarin mulkin dimokuraɗiyya, dangantaka tsakanin bangaren zartarwa da majalisun dokoki tana taka muhimmiyar rawa wajen gudanar da shugabanci a tsakanin al’umma.

A galibin kasashe masu bin tsarin na dimokuraɗiyya, ’yan majalisa kan kasance masu wakiltar al’umma da kare muradunta, da sa ido da kuma bayar da shawarwarin da suka dace ga bangaren zartarwa domin ci-gaban kasa.

Sai dai a Najeriya, a wasu lokutan akan zargi ’yan majalisa da zama ’yan-amshin-Shata.

Ko me ya sa haka? Shin yaya ya kamata dangantaka ta kasance a tsakanin bangaren zartarwa da majalisar dokoki a tsarin mulkin dimokuraɗiyya?

NAJERIYA A YAU: Dalilin ’Yan Adawa Na Ƙulla Ƙawance A Ƙarƙashin Inuwar ADC DAGA LARABA: “Abba Al-Mustafa Ba Shi Da Hurumin Dakatar Da Fina-finanmu”

Wannan shi ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai duba.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Majalisar Dokoki Majalisar Zartarwa

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: Obi ya ziyarci iyalin Ɗantata don yi musu ta’aziyya

Ɗan takarar Shugaban Ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Peter Obi, ya ziyarci iyalin marigayi, Alhaji Aminu Dantata a Jihar Kano, don yi musu ta’aziyya.

Obi, ya bayyana cewa ya yi matuƙar baƙin ciki da rasuwar Alhaji Ɗantata, inda ya bayyana shi a matsayin “uba ga kowa.”

An gabatar da Ganduje a matsayin shugaban kwamitin hukumar FAAN 2027: Idan ADC na son lashe zaɓe dole ta bai wa ɗan Arewa takara — Okonkwo

Ya yaba yadda Ɗantata ya zama babban attajiri kuma ya taimaka wa mutane da dama suka samu nasara a rayuwarsu.

Ya ce Ɗantata ya taka muhimmiyar rawa wajen ci gaban Najeriya.

“Mun zo nan yau don jimami tare da iyalinsa da kuma ɗaukacin ‘yan Najeriya, saboda wannan babban rashi ne,” in ji Obi.

“Alhaji Aminu Dantata ba mai kuɗi ba ne kawai, ya taimaka wa wasu wajen cimma nasararsu a rayuwa.

“Ya kula da mutane sosai kuma ya zama kamar uba ga mutane da dama.”

Obi, ya bayyana Ɗantata a matsayin mutum mai tausayi da kishin ƙasa.

Ya ce mutuwarsa ta shafu al’amura da dama a wannan zamani.

Haka kuma, Obi ya yi addu’ar Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta masa, ya saka masa da alheri, ya kuma albarkaci iyalinsa.

“Rayuwarsa abin koyi ce. Ba wai kasuwanci kawai ya yi ba, ya zuba jari a cikin al’umma. Abin da ya bari zai ci gaba da zama abin koyi.

“Allah Ya albarkaci wannan gida, ya albarkaci Najeriya baki ɗaya,” in ji Obi.

Alhaji Aminu Ɗantata fitaccen ɗan kasuwa ne luma mai taimakon jama’a daga Arewacin Najeriya.

Ya rasu yana da shekarau 94.

Mutane da dama daga sassa daban-daban na ƙasar nan sun yi alhini bisa gudunmawar da ya bayar a harkar tattalin arziƙi da taimakon jama’a.

Ga hotunan ziyarar a ƙasa:

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Muna tunanin sayar da matatun man Najeriya — NNPCL
  • Ya kamata mulkin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ’yan Kudu — Hannatu Musawa
  • Ba lallai matatun man gwamnati su sake aiki ba har abada a Najeriya – Ɗangote
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Wasu Matasa Ba Sa Aiki Tukuru Wajen Neman Arziki
  • NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Cin Kifi Yadda Ya Kamata
  • Aragchi Ya Tattauna Da Bin Salman Kan Karfafa Zumunci Tsakanin Kasashen Biyu
  • HOTUNA: Obi ya ziyarci iyalin Ɗantata don yi musu ta’aziyya
  • Biza: UAE ta ƙaƙaba wa ’yan Najeriya sabbin takunkumai
  • Iran Ta Musanta Neman Ci Gaba Da Gudanar Da Tattaunawa Da Amurka Kan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba