Sojojin Yemen Zasu Bullo Da Shirin Takurawa Jiragen Saman Haramtacciyar Kasar Isra’ila
Published: 31st, May 2025 GMT
Dakarun gwagwarmayar kasar Yemen sun bayyana cewa: Za su mayar da jiragen saman yakin gwamnatin mamayar Isra’ila abin ba’a
Shugaban majalisar koli ta siyasar kasar Yemen Mahdi al-Mashat, ya tabbatar da cewa: Tsaron sararin samaniyar sojojin kasar Yemen zai iya tunkarar jiragen saman yakin gwamnatin mamayar Isra’ila da suke kai hare-haren wuce gona da iri kan kasar Yemen.
Shugaban majalisar koli ta siyasar kasar Yemen Mahdi al-Mashat ya shaidawa tashar talabijin ta Al-Mayadeen cewa: Kariyar tsaron sararin samaniyar sojojin Yemen za ta mayar da jirgin saman makiya ‘yan sahayoniyya abin izgili a cikin kwanaki masu zuwa.
Al-Mashat ya jaddada cewa: Sojojin kasar Yemen za su iya tunkarar jiragen saman yakin yahudawan sahayoniyya ba tare da haifar da wata illa ga zirga-zirgar jiragen sama da na ruwa ba,” yana mai cewa “labarin farin ciki da ke matsayin albishir” zai zo da zai zama ana murkushe jiragen saman makiya yahudawan sahayoniyya da suke amfani da shi wajen kai farmaki kan kasar Yemen.
Shugaban majalisar koli ta siyasar kasar Yemen ya yi ishara da cewa: An bayyana hanyoyin da makiya yahudawan sahayoniyya suke kaiwa kasar Yemen a matsayin wurare masu hadari ga dukkanin kamfanoni, domin tabbatar da tsaron zirga-zirgar jiragen sama da na ruwa a yankunan da sojojin kasar ke gudanar da ayyukansu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: jiragen saman kasar Yemen
এছাড়াও পড়ুন:
Aragchi: Shirin Nukliyar Kasar Iran Na Tafiya Kan Fahintar Rashin Amincewa Da Babakere
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa JMI ta gina shirinta na makamashin nukliya ne kan fahinta da kuma kundin tsarin mulkin kasar wanda yayi tir da mamaya da kuma babakere.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a safiyar yau Asabar a hubbaren Imam Ruhullah Al-khomaini (q) wanda ya kafa JMI. Ministan da sauran manya-manyan ma’aikata a ma’aikatar harkokin wajen kasar sun je hubbaren Imam ne don jadda bai’a ko alkawali da shi kan tafiya a kan tafarkin da ya barsu a kai.
A cikin wani wuri a Jawabinsa Ministan ya kara da cewa a cikin kundin tsarin mulkin JMI ya zo kan cewa Iran ba zata danne wata kasa ba kuma ba zata amince da danniyaba, hakama ba zata zalunci wata kasa ba kuma ba zata yarda a zalunceta ba.
Ya ce abinda gwamnatin kasar Amurka take son tayiwa JMI shi ne danniya da zalunci, Kalmar kada ku ce makamacin Uranium kanta danniya ce. Su sun amincewa kansu su mallaki makaman nukliya amma ba zasu amincewa wata kasa ta ma tashe makamashin uranium wanda yarjeniyar NPT ta amince masu su tace ba. Don haka wannan baa bin amincewa ne ga JMI ba.