Sojojin Yemen Zasu Bullo Da Shirin Takurawa Jiragen Saman Haramtacciyar Kasar Isra’ila
Published: 31st, May 2025 GMT
Dakarun gwagwarmayar kasar Yemen sun bayyana cewa: Za su mayar da jiragen saman yakin gwamnatin mamayar Isra’ila abin ba’a
Shugaban majalisar koli ta siyasar kasar Yemen Mahdi al-Mashat, ya tabbatar da cewa: Tsaron sararin samaniyar sojojin kasar Yemen zai iya tunkarar jiragen saman yakin gwamnatin mamayar Isra’ila da suke kai hare-haren wuce gona da iri kan kasar Yemen.
Shugaban majalisar koli ta siyasar kasar Yemen Mahdi al-Mashat ya shaidawa tashar talabijin ta Al-Mayadeen cewa: Kariyar tsaron sararin samaniyar sojojin Yemen za ta mayar da jirgin saman makiya ‘yan sahayoniyya abin izgili a cikin kwanaki masu zuwa.
Al-Mashat ya jaddada cewa: Sojojin kasar Yemen za su iya tunkarar jiragen saman yakin yahudawan sahayoniyya ba tare da haifar da wata illa ga zirga-zirgar jiragen sama da na ruwa ba,” yana mai cewa “labarin farin ciki da ke matsayin albishir” zai zo da zai zama ana murkushe jiragen saman makiya yahudawan sahayoniyya da suke amfani da shi wajen kai farmaki kan kasar Yemen.
Shugaban majalisar koli ta siyasar kasar Yemen ya yi ishara da cewa: An bayyana hanyoyin da makiya yahudawan sahayoniyya suke kaiwa kasar Yemen a matsayin wurare masu hadari ga dukkanin kamfanoni, domin tabbatar da tsaron zirga-zirgar jiragen sama da na ruwa a yankunan da sojojin kasar ke gudanar da ayyukansu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: jiragen saman kasar Yemen
এছাড়াও পড়ুন:
Eritrea ta gargadi Habasha game da yunkurin kafa tashar jiragen ruwa a cikin yankinta
Wata sabuwar tashin-tashina ta sake kunno kai a yankin kahon Afirka a daidai lokacin da shugaban kasar Eritrea Isaias Afwerki ya yi gargadi kai tsaye ga firaministan Habasha Abiy Ahmed, inda ya yi kashedin sake kaddamar da wani yaki.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da kasar Habasha ke kokarin shiga bangaren ruwa Eritra da kuma tabarbarewar dangantakar bangarorin biyu tun bayan rikicin Tigray.
A cikin wani jawabi da ya yi ta gidan telebijin, shugaba Afwerki ya yi gargadin cewa adadin yawan jama’ar Habasha ba zai tabbatar da nasarar soji ba, yana mai nuni da dabarun yakin da Habasha ta yi amfani da su a yakin da ya gabata, yana mai cewa duk da yawan sojojinta amma bata samu nasara ba.
Afwerki ya kira matakin na Abiy a matsayin “rashin hankali” tare da danganta hakan da matsalolin siyasar cikin gidan Habasha. Ya kuma nanata cewa Eritrea ba za ta amince da keta hurumin kasarta ba, ya kuma bukaci Habasha da ta warware matsalolin cikin gida kafin ta yi la’akari da daukar mataki a kan waje.
Kasar Habasha wadda ita ce kasa mafi yawan al’umma a gabashin nahiyar Afirka, ta dade tana neman shiga Tekun Bahar Maliya, ayyin da Eritiriya take yin matukar kaffa-kaffa da wannan manufa ta Habasha.
Kasashen Eritrea da Habasha sun jima suna zaman doya da manja tun bayan da Eritrea ta kwashe shekaru 30 tana yakin neman ‘yencin kai da mulkin Habasha, wanda ya kai ga samun ‘yancin kai a 1993.
Rikicin da ya fi kamari ya faru ne daga 1998 zuwa 2000, lokacin da wani mummunan yakin kan iyaka ya yi sanadin mutuwar mutane sama da 100,000. Duk da yarjejeniyar zaman lafiya da aka sanya hannu a kanta a cikin 2018, amma babu wani tabbaci kan ci gaba da wanzuwar wannan yarjejeniya.
Habasha tana da yawan jama’a miliyan 130, Eritrea miliyan 3.5 kawai.