Leadership News Hausa:
2025-11-02@06:25:17 GMT

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

Published: 31st, May 2025 GMT

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

Karatu, rubutu,da kuma dabarun lissafi wasu dabaru ne da ake samu ta hanyar iulimi. Wadannan dabarun suna bada dama ta dogaro da kai da kuma samarwa kai aiki.

Karatu yana bude hanyar sanin ilimi da labarin duniya. Saboda mutane suna fara kasuwanci ne idan har za su iya kasafi,da kuma gane abubuwan da aka kashe a kalla.

Ilimin iya karatu da rubutu,da kuma iya samar da hanayar da za aji ra’ayoyi,hakan na kara iya dogaro da kai da kuma samun a rika jin babu wata kasala ko faduwar gaba.

Ilimi yana taimakawa mutane wajen yadda wasu daga zama Sanuwar ware.

Yin makaranta yana koyawa mutane duk wani matakin da za su dauka ya kasance mai ma’ana, wannan kuwa yana sa su shirya lamarin zama matasa,da kuma cikakken mutum, inda duk wani matakin da za’a dauka kowace rana, babba, ko karami zai kasance wani bangare ne na rayuwar su matasan.

Gwargwadon ilimin mutum gwargwadon irin kudin albashin da zai samu.Idan aka samu ilimi maiinganci sau da yawa ko mafi akasari ya kan yi sanadiyar samun aikin da za a rika biyan albashi mai tsoka,da samar da wasu dabaru da suka zama da’iman suna da muhimmanci.

Yana samar da hanyar rayuwa mai sauki, wadda babu wanda ya isa ya dauka elamarin daga wurin kai mai ilimin,. Idan muna da ilimi,wani abu ne wanda namu ne kadai,wanda hakan yana bamu damar mu tsaya da kafafunmu.

Ilimi yana koyawa mutane yadda za su yi tunani sosai har ila yau kuma a cikin tsari,bayanan kuma su yi alkalanci mai hujja ba tare da shawara da wani ba.Matsalolin da ake iya fuskanta idan an fara/ko anyi girma sunesun hada da biyan basuksukan da aka dauka lokacin makaranta,samun aikin yi,sayen gida,da kuma iaya daukar dawainiya ko nauyin iyali.Wadanda suka yi shekaru suna makaranta/karatu,irin su,suna iya yin tunani ko daukar matakai wadanda zasu taimaka masu wajen su matsalolin da aka bayyana.

Abin ya danganta ne ga irin burin da mutum yayi niyyar cimmawa, idan aka yi karatu mai zurfi sosai, yana taimakawa wanda ya yi karatun cimma dukkannin abubuwan da yasa a gabansa.

Ilimi yana kara rayuwa mai tsawo saboda nazarin da aka yi ya nuna kowace shekarar ilimi, ilimi yana kara shekara 1.7 ga mutane lokacin da suka kai shekara 35 cewar.(Lleras-Muney, 2005)

Ilimi yana da matukar muhimmanci ga ci gaban Dan Adam.

Ilimi yana taimakawa mutane su gane ko su, su wanene. Suna iya sanin kansu ta hanyar Littattafai, kwasa- kwasai, har ma da irin shawarar da kwararru.

Ilimi yana bada damar yadda mutane za su san duniya abinda ake ciki,sai kuma su wanene kusa da su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani

Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani, ya soki Shugaban Amurka, Donald Trump, bisa kiran Najeriya “ƙasa mai matsala ta musamman” kan zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi.

Sani, ya ce kalaman Trump sun samo asali ne daga bayanan da ba su da tushe, da wasu mutane suka ba shi domin su tayar da fitina a Najeriya.

Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia ta yi tazarce da kashi 97 an ƙuri’u

A ranar Juma’a ne, Trump ya wallafa rubutu a shafinsa na sada zumunta cewar Kiristanci yana cikin hatasri a Najeriya.

Ya yi iƙirarin cewa ’yan ta’adda sun kashe dubban Kiristoci, amma ya ce Amurka za ta yi duk mai yiwuwa wajen “ceto Kiristoci” a Najeriya da wasu ƙasashe.

Shehu Sani, ya mayar da martani da cewa wannan magana ba gaskiya ba ce, domin matsalar tsaro a Najeriya ba ta da nasaba da addini.

Ya ce Musulmai da Kiristoci dukkaninsu suna fuskantar hare-haren’yan ta’adda da garkuwa da su.

“Wannan zargi ƙarya ne. ’Yan ta’adda da ’yan bindiga a Najeriya suna kashe mutane ba tare da la’akari da addininsu ba. Wannan abin na faruwa tun kusan shekaru 15 da suka wuce,” in ji shi.

Sani, ya ƙara da cewa, saboda yawan Musulmai da Kiristoci a Najeriya, ba zai yiwu addini ɗaya ya zalunci ɗaya ba.

“Idan aka duba yadda Musulmai da Kiristoci suke kusan daidai a Najeriya, ba zai yiwu ɗaya ya zalunci ɗaya ba. Najeriya kamar zaki da damisa ce, dukkanin ɓangarorin suna da ƙarfi,” in ji shi.

Ya zargi waɗanda suka zuga Trump da amfani da rikice-rikicen cikin gida na Najeriya.

“Trump ya samu bayanan ƙarya daga mutanen da ke son raba Najeriya domin su ci moriya daga wannan,” in ji shi.

“Wannan makirci da aka yi wa ƙasar nan ba zai yi nasara ba.”

Sani, ya roƙi ƙasashen duniya su taimaka wa Najeriya wajen yaƙar ta’addanci, maimakon yaɗa labaran ƙarya.

“Najeriya na buƙatar taimako da haɗin kai wajen shawo kan matsalar tsaro, kamar sauran ƙasashen da ke fama da ta’addanci,” a cewarsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu
  • Kungiyar Rapid Support Forces Ta Sanar Da Kafa Kwamitin Bincike Kan Cin Zarafin Al’umma A El Fasher