Leadership News Hausa:
2025-07-26@08:00:44 GMT

Taron Kolin ASEAN Sin Da GCC Na Da Matukar Muhimmanci

Published: 28th, May 2025 GMT

Taron Kolin ASEAN Sin Da GCC Na Da Matukar Muhimmanci

Ra’ayoyi daga sassan kasa da kasa sun karkata ga muhimmancin taron kolin ASEAN-Sin-GCC karo na farko da ya gudana a birnin Kuala Lumpur fadar mulkin kasar Malaysia a jiya Talata 27 ga watan nan.

Daga mahanga ta shiyya, taron bangarorin uku ya mayar da hankali ga manyan sassa uku, wadanda suka hada da gabashin Asiya, da kudu maso gabashin Asiya da yankin Middle East, tare da cewa ba kasafai ake samun irin wannan hadin gwiwar shiyyoyi a yankin Asiya ba.

A gabar da ake fuskantar tarin kalubale a matakin kasa da kasa masu matukar sarkakiya, da raunin bunkasar tattalin arzikin duniya, Sin da ASEAN da GCC na aiki tare domin gina da’irar tattalin arziki ta bai daya da ci gaba tare. Hakan ba kawai zai amfani tattalin arzikin sassan ba ne, har ma zai ingiza yanayin zaman lafiya, da ci gaba a Asiya da ma sauran sassan duniya baki daya.

Sin da kasashe mambobin ASEAN, da na GCC dukkanin su suna da muhimmanci cikin jerin kasashe masu tasowa. Wannan taron koli na hadakar sassa uku ya mayar da hankali ga zakulo sabon tsarin hadin gwiwar shiyyoyi tsakanin kasashe masu tasowa, wanda hakan ke da matukar muhimmanci. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa Sun Gamsu Zuba Jari A Sin Dama Ce Ta Cimma Nasarar More Riba A Nan Gaba

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Miliyoyin Al’ummar Yemen Sun Fito Taron Gangamin Nuna Goyon Baya Ga Falasdinawa
  • Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa
  • Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka
  • 2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku
  • Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD
  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU
  • Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 
  • Kungiyar “Human Right Watch” Ta Yi Kira Da A Saki Tsohon Shugaban Kasar Nijar Muammad Bazoum
  • Iran: Iran Tana Cikin Kasashe Biyar Na Duniya Da Suka Ci Gaba Wajen Kiwon Dabbobi
  • Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa Sun Gamsu Zuba Jari A Sin Dama Ce Ta Cimma Nasarar More Riba A Nan Gaba