Kasar Iran, Da Kasashen Kungiyar BRICS Sun Gudanar Da Taro Kan Harkokin Tsaro A Mosco
Published: 29th, May 2025 GMT
An ngudanar da taron harkokin tsaro na kungiyar BRICS karo na 13TH inda wakilai da kasashen Iran da sauran kasashen kungiyar a birnin Mosco a ranar Laraba 28 ga watan Mayun da muke ciki.
Shafin yanar gizo na labarai AfricaNews ya bayyana cewa babbakan sakataren majalisar tsaro na kasar Iran Ali Akbar Ahmadian da Shugaban Bosnina serb Milorad Dodik da ministan tsaron kasar Korea ta Arewa Ri Chang-dae da kuma da wakilan tsaro daga kasashen duniya fiye da 100 ne suka sami halattan tarom na kwana guda.
A gefen taron a jiya Laraba sakataren majalisar tsaro na kasar Rasah Sergei Shoigu ya gana da tokwaransa na kasar Iran Ahmadian inda suka tattauna kan al-amura da suka shafe harkokin tsaro tsakanin kasashen biyu.
An gudanar da taron ne daga 27-29 ga watan Mayu da muke ciki sannan wakilai 126 ne suka halarci taron.daga kasashen 104 wadanda suka kasance mambobi a kungiyoyin BRICS,Sco,ASEAN CIS da kuma kasashen kungiyar kasashen Larabawa , Au CSTO da wasu kungiyoyin kasa da kasa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Iran na ziyarar aiki a kasar Oman
Shugaban kasar Iran, Massoud Pezeshkian, ya fara wata ziyarar aiki a kasar Oman mai manufar karfafa dangantaka tsakanin kasashen biyu aminnan juna.
Shugaba Pezeshkian ya yaba da rawar da Oman ta taka a tattaunawar dake tsakanin Iran da Amurka, kuma tana fatan za a cimma sakamako mai kyau.
Pezeshkian ya bayyana hakan ne yayin ganawa da ya yi da Sultan Haitham bin Tariq na Oman a birnin Muscat a yammacin yau Talata.
Da yake jaddada matsayin kasar Oman a cikin manufofin ketare na Iran, Pezeshkian ya ce Tehran na da cikakkiyar amincewa ga Oman, kuma wannan amana na karfafa alaka tsakanin kasashen biyu.
Shugaban ya ce Iran a shirye ta ke ta inganta hadin gwiwa da Oman a dukkan fannoni, yana mai imani cewa kasashen biyu suna da karfin da za a iya amfani da su don cin moriyar juna da sauran al’ummomin yankin,” in ji shi.
Ya ce Iran a shirye take ta inganta hadin gwiwa da Oman a fannonin, kimiyya, ilimi, da fasaha, musamman a fannin likitanci.
A nasa bangare Sultan Haitham ya bayyana cewa ya yarda idan aka bude hanyoyin gudanar da harkokin kasuwanci, kasashen biyu za su samu gagarumin ci gaba a huldar dake tsakaninsu.
Dangane da tattaunawar dake tsakanin Iran da Amurka, Sultan Haitham ya ce Muscat ta shiga tsakani a tattaunawar da alheri,” in ji shi.
Sarkin na Oman ya kuma yaba da matsayin Iran na kare al’ummar Falasdinu.