Kunngiyar Tarayyar Turai, ta ce ba ta gamsu da sabon tsaron raba kayan agajin jin kai da Amurka da Isra’ila ke shirin aiwatarwa a Gaza.

Babbar jami’ar diflomasiyyar kungiyar, Kaja Kallas, ta bayyana cewa Tarayyar Turai ba ta goyon bayan sabon tsarin raba agajin jin kai da Amurka da Isra’ila ke kokarin aiwatarwa wanda ke kaucewa hadin gwiwa da Majalisar Dinkin Duniya da sauran kungiyoyin agaji.

Kallas, ta kuma bayyana cewa hare-haren da Isra’ila ke kai wa a Gaza sun wuce abun da suke bukata wajen yakar Hamas, a yayin da adadin wadanda suka rasa rayukansu ke ci gaba da karuwa.

Tun bayan da Isra’ila ta dawo da yaki a watan Maris bayan ruguza  yarjejeniyar tsagaita wuta da ta cimma da Hamas, kimanin mutum 3,924 ne sukayi shahada a cewar ma’aikatar lafiyar a Gaza.

Isra’ila dai ta ci gaba da cewa tana kai hare-haren ne don kawar da Hamas da ceto wadanda kungiyar ke garkuwa da su.

Sai dai hare-haren kwanan nan sun yi sanadin mutuwar fararen hula da dama.

Jawabin Kallas ya biyo bayan kalamman da Firaministan Jamus, Friedrich Merz, ya yi, inda ya bayyana cewa “a yanzu ba ya fahimtar manufar Isra’ila a Gaza.”

Isra’ila dai ta fara kai farmaki a Gaza ne bayan harin ba zata na Hamas a ranar 7 ga Oktoban 2023, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane akalla 1,200 da kuma sace wasu 251, sai kuma mutane sama da 54,084 a hare-haren ramuwar gayya na Isra’ila.  

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: da Isra ila

এছাড়াও পড়ুন:

Ko Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Trump Ya Gujewa Yaki Da Yemen Har Ya Kai Ga Fusata Kawayen Amurka

Gujewar da Trump ta yi daga yakin Yemen ya harzuka mahukuntan gwamnatin Isra’ila da kasashen Larabawa da suka dogara da shi

Shafin Jaridar Hill ta Amurka ta buga wani sabon labarin da ke bayyana irin kayen da Amurka ta sha a Yemen da kuma irin dimbin hasarar da Amurkan ta yi domin kare yahudawan sahayoniyya kafin ficewa daga kangin matakin martanin kasar Yemen.

Labarin da Imran Khaled ya rubuta mai taken “(Al’ummar Yemen) sun yi tsayin daka da kuma ja da baya da Trump ya yi… Shin Amurka za ta fice daga Yemen?”, yarjejeniyar “dakatar da kai hare-haren wuce gona da irin Amurka kan Yemen” ta bayyana yadda Amurka ta yin watsi da kawayenta cikin sauki, wanda ke nufin gwamnatin ‘yan sahayoniya.

Ya yi nuni da cewa: Barin harin wuce gona da iri kadai a gaban ci gaba da ayyukan Yemen, yana kara karfafa labarin kasar Yemen da suke gabatar da tallafi da taimako a kodayaushe ga gwamnatocin Larabawa da na Musulunci, da hakan ke fayyace cewa Amurka ba abar dogaro ba ce, kuma cikin sauri ta yi watsi da “kawayenta” wanda hakan ya faru a zahiri bayan ficewar Amurka daga “yakin kare yahudawan sahayoniyya”.

Ya bayyana cewa: Mai laifi Trump ya kwatanta mutanen Yemen a matsayin jarumai da masu juriya, bayan da a baya ya yi barazanar “murkushe su baki daya” ya nuna cewa shugaban na Amurka ya mika wuya tare da ayyana shan kaye, amma yana shelanta cewa ya yi nasara, yana mai jaddada cewa sakamakon yakin ya tabbatar da rashin nasara ga Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Falasdinawa 23 Suka Yi Shahada A Farmakin Da Sojojin Mamayar Isra’ila Suka Kai Kan Sansanin Al-Bureij
  • ‘Yan Tawayen Sudan Sun Kashe Fararen Hula 10 A Hare-Haren Da Suka Kai Kan Birnin Kordofan
  •  Fiye Da Falasdinawa 60 Ne Su Ka Yi Shahada A Jiya Laraba
  •  Yemen: Wuce Gona Da Irin HKI Ba Zai Sauya Mana Ra’ayi Akan Ci Gaba Da Taimaka Wa Gaza Ba
  •  Kasar Chile Na Shirin Yanke Alakar Diplomasiyya Da “Isra’ila”
  • Tashin Hankali A Gaza Bayanda HKI Ta Bude Rumbun Ajiyar Kayakin Agaji A Rafah
  •  Falasdinawa Da Dama Sun Yi Shahada A Zirin Gaza
  • Ko Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Trump Ya Gujewa Yaki Da Yemen Har Ya Kai Ga Fusata Kawayen Amurka
  • Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Wa Yankunan Gaza Hare-hare