A tsawon kwanaki 602 a jere, sojojin mamayar Isra’ila suna ci gaba da aiwatar da kisan kiyashi kan Falasdinawa a yankin Zirin Gaza

Sojojin mamayar Isra’ila na ci gaba da yakin da suke yi na kisan kiyashi a zirin Gaza, inda suka sake kaddamar da wani sabon yaki kan Gaza bayan tsagaita bude wuta. Hakan ya biyo bayan sauya ra’ayi da Fira ministan gwamnatin haramtaciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu ya yi kan yarjejeniyar tsagaita bude wuta, bisa la’akari da goyon bayan siyasa da na soji da Amurka ke ba shi, a cikin shiru da kasashen duniya suka yi da kuma gazawar da ba a taba gani ba daga kungiyoyin kasa da kasa.

Kafofin yada labaran Falasdinu sun ruwaito cewa: Sojojin mamayar Isra’ila sun kaddamar da jerin hare-hare ta sama kan yankunan Gaza,                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                     da nufin tsaurara tasirin hana shigar da kayan abinci da ya karu tun farkon watan Maris. Wannan ya ba da mummunan hoto na yunwar da mazauna Gaza ke fuskanta.

A safiyar yau Juma’a, jiragen saman yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila suka kaddamar da wani mummunan farmaki kan yankunan kudancin Khan Yunus. Kamar yadda sojojin na Isra’ila suka yi luguden wuta kan sansanin ‘yan gudun hijira na Al-Bureij da ke arewacin zirin Gaza da kuma arewa maso yammacin Rafah.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Yemen Sun Hana Jigilar Jiragen Sama A Isra’ila Tare Da Firgita ‘Yan Sahayoniyya

Sojojin Yemen sun kai hari kan filin jirgin saman Ben Gurion da makami mai linzami lamarin da ya tarwatsa cinkoson jama’a a filin jirgin

Sojojin Yemen sun sanar da kai farmakin soji kan filin tashi da saukan  jiragen saman Ben Gurion tare da yin barazanar ci gaba da toshe hanyoyin zirga-zirgar jiragen sama da na ruwa na haramtacciyar kasar Isra’ila muddin bata kawo karshen killace Zirin Gaza da ta yi ba.

Kakakin rundunar sojin kasar Yemen Birgediya Janar Yahya Sari’e ya tabbatar da cewa: Wannan farmakin ya samu nasarar cimma burin da aka sanya a gaba, wanda ya tilastawa miliyoyin ‘yan sahayoniyya ‘yan mamaya tserewa zuwa maboyar karkashin rami tare da dakatar da zirga-zirgar jiragen sama a filin jirgin.

Sari’e ya kara da cewa: Wannan farmakin yana tabbatar da ci gaba da gudanar da ayyukan sojojin Yemen na wajibin addini, kyakkyawar dabi’a da jin kai da kuma dan Adamtaka ga ‘yan uwansu na Falastinu har sai an daina kai hare-haren wuce gona da iri kan Falasdinawa da killace su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Ambaliyar Garin Mokwa A Neja
  • ‘Yan Gwagwamayar Falasdinu Sun Halaka Sojojin Mamayar Isra’ila Masu Yawa A Wani Harin Kwanton Bauna
  • Sojojin Yemen Zasu Bullo Da Shirin Takurawa Jiragen Saman Haramtacciyar Kasar Isra’ila  
  • Burkina Faso ta musanta zargin kisan kiyashi da ake yi a arewacin kasar
  • Sojojin Yemen Sun Hana Jigilar Jiragen Sama A Isra’ila Tare Da Firgita ‘Yan Sahayoniyya
  • Falasdinawa 23 Suka Yi Shahada A Farmakin Da Sojojin Mamayar Isra’ila Suka Kai Kan Sansanin Al-Bureij
  • Kungiyar ASEAN Ta Bayyana Damuwarta Da Kissan Kiyashi A gaza
  •  Fiye Da Falasdinawa 60 Ne Su Ka Yi Shahada A Jiya Laraba
  • Gaza : EU ba ta gamsu da sabon tsarin raba agaji na Amurka da Isra’ila ba