Gujewar da Trump ta yi daga yakin Yemen ya harzuka mahukuntan gwamnatin Isra’ila da kasashen Larabawa da suka dogara da shi

Shafin Jaridar Hill ta Amurka ta buga wani sabon labarin da ke bayyana irin kayen da Amurka ta sha a Yemen da kuma irin dimbin hasarar da Amurkan ta yi domin kare yahudawan sahayoniyya kafin ficewa daga kangin matakin martanin kasar Yemen.

Labarin da Imran Khaled ya rubuta mai taken “(Al’ummar Yemen) sun yi tsayin daka da kuma ja da baya da Trump ya yi… Shin Amurka za ta fice daga Yemen?”, yarjejeniyar “dakatar da kai hare-haren wuce gona da irin Amurka kan Yemen” ta bayyana yadda Amurka ta yin watsi da kawayenta cikin sauki, wanda ke nufin gwamnatin ‘yan sahayoniya.

Ya yi nuni da cewa: Barin harin wuce gona da iri kadai a gaban ci gaba da ayyukan Yemen, yana kara karfafa labarin kasar Yemen da suke gabatar da tallafi da taimako a kodayaushe ga gwamnatocin Larabawa da na Musulunci, da hakan ke fayyace cewa Amurka ba abar dogaro ba ce, kuma cikin sauri ta yi watsi da “kawayenta” wanda hakan ya faru a zahiri bayan ficewar Amurka daga “yakin kare yahudawan sahayoniyya”.

Ya bayyana cewa: Mai laifi Trump ya kwatanta mutanen Yemen a matsayin jarumai da masu juriya, bayan da a baya ya yi barazanar “murkushe su baki daya” ya nuna cewa shugaban na Amurka ya mika wuya tare da ayyana shan kaye, amma yana shelanta cewa ya yi nasara, yana mai jaddada cewa sakamakon yakin ya tabbatar da rashin nasara ga Amurka.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin da ya sa muka gayyaci Sheikh Lawal Triumph – ’Yan sanda

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta bayyana dalilin da ya sa ta gayyaci malamin addini Sheikh Lawal Triumph.

A wata sanarwa da ta fitar, ’yan sanda sun ce sun sani cewa wasu daga cikin wa’azozin da Sheikh Triumph ke yi suna haddasa rashin jituwa a tsakanin al’ummar jihar.

Ya kamata mulkin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ’yan Kudu — Hannatu Musawa Ba lallai matatun man gwamnati su sake aiki ba har abada a Najeriya – Ɗangote

Rundunar ta ce kowa na da ’yancin faɗin albarkacin bakinsa, amma dole ne komai ya kasance bisa doka.

Saboda haka ne Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, ya gayyaci Sheikh Lawal Triumph don tattaunawa da jami’an gwamnati, shugabannin addini da na al’umma.

Manufar ita ce a nemi hanyar hana irin wannan rikici sake faruwa a nan gaba.

Rundunar ta kuma buƙaci al’umma da su kwantar da hankalinsu su guji yin abubuwan da za su haifar da tashin hankali.

“Yana da muhimmanci a girmama ra’ayin juna da abin da mutane suka gaskata, kuma a tabbatar da cewa duk abin da mutum zai faɗa ko zai yi bai saɓa wa doka ba,” in ji rundunar.

Wannan lamari ya fara ne bayan wani wa’azi da Sheikh Lawal Triumph ya yi, wanda ya tayar da ƙura.

Ya faɗi haka ne a matsayin martani ga waɗanda suke musanta wani hadisi da ke cewa kwarkwata ƙazanta ce.

Wannan ya janyo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, inda wasu suka fara kiran a kashe Sheikh Lawal Triumph bisa zargin ya yi izgili ya Manzon Allah (S.A.W).

Rundunar ta kuma shawarci jama’a da su kai koken su ga hukumomin da suka dace, maimakon yaɗa saƙonni da za su iya tayar da hankali a shafukan sada zumunta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Tana Nazarin Sakon Amurka Na Bukatar Farfado Da Tattaunawa Shirin Makamashin Nukliya Na kasar
  • NYT: Natanyahu Yana Tsawaita Yaki A Gaza Don Ci Gaba Da Kasancewa Kan Iko A HKI
  • Lavrov: Shuwagabannin Kasashen Yammacin Turai Suna Son Shiga Yaki Da Rasha
  • Dalilin da ya sa muka gayyaci Sheikh Lawal Triumph – ’Yan sanda
  • HKI Ta Roki Amurka Ta Taimake Ta A Fada Da Kasar Yemen
  • Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista
  • Qalibof: Asarorin HKI A Yakin Kwanaki 12 Yafi Abinda Ta Bayyana
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci  ya Bayyana Yadda Iran Da Mayar Da Martani Mai Gauni Kan Isra’ila
  • Yemen Ta Nutsarda Wani Jirgin Ruwana HKI Saboda Sabawa Haramcin Wucewa Ta Red Sea
  • Trump Ya Kakabawa Wata Jami’in MDD Takunkumi Bayan Ta Fallasa Laifukan HKI Da Hannun Amurka A Ciki