Sojojin HKI Sun Yi Wani Sabon Kisan Kiyashi A Gaza
Published: 26th, May 2025 GMT
Hare-haren sojojin HKI a yankin Gaza sun yi sanadiyyar shahadar Falasdinawa 57
Majiyar Asibiti a yankin na Gaza,ta sanar da cewa sojojin mamayar sun kai hari ne akan makarantar ” Fahmi al-jarjawi” wacce take a yankin al-Darj’ a cikin birnin Gaza, da hakan ya yi sanadiyyar shahadar Falasdianwa 25.”
Harin ya yi sanadiyyar konewar gawawwakin shahidan da kuma tashin gagarumar gobara a makarantar da ‘yan hijira Falasdinawa suke ciki.
Ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta sanar da cewa daga 7 ga watan Oktoba 2023 zuwa yanzu adadin shahidan Falasdinawa ya haura dubu 53 da 939.
Haka nan ma’aikatar ta ce; Wadanda su ka jikkata kuwa a wannan tsakanin sun kai dubu 122 da 797.
Sojojin HKI sun shelanta yaki ne akan yankin Gaza da zummar murkushe kungiyar Hamas, sai kuma kwato fursunonin da suke hannun ‘yan gwagwarmaya, lamarin da ya zuwa yanzu babu wanda ya tabbata.
Daga farkon yakin ne dai kungiyar Hamas ta sanar da cewa, ta hanyar tattaunawa ne kadai za a iya yin musayar fursunoni.
Ya zuwa yanzu kuwa an yi musayar fursunonin a tsakanin bangarorin biyu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila ta kashe Falasdinawa 24 a Zirin Gaza
Sojojin Isra’ila sun kashe Falasdinawa 24 daga cikin dare zuwa wayewar garin ranar Alhamis a Zirin Gaza.
Majiyoyi a yankin sun shaida wa gidan talabijin na Al-Jazeera cewa akasarin mutum 24 din da aka kashe a zirin na Gaza mata ne da kananan yara.
NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Cin Kifi Yadda Ya Kamata Ba Tinubu kaɗai ne ya sa Buhari ya ci zaɓe a 2015 ba – Boss MustaphaAkasarin mutanen dai an kashe su ne a tsakiya da kudancin zirin na Gaza.
Ma’aikatan lafiya a asibitin Al-Aqsa da ke Gaza sun ce a yankin Deir el-Balah kawai akwai Falasdinawa 13 da aka kashe sannan an jikkata wasu da dama.
Gabanin nan ma, Isra’ila ta kashe mutum hudu a harin da ta kai sansanin ’yan gudun hijira na Bureij, shi ma wanda ke tsakiyar Gaza.
Sama da mutum 700 ne Isra’ila ta kashe Falasdinawa 700 da ke kokarin karbar tallafi a wuraren karbar tallafi na Gidauniyar GHF wanda Amurka da Isra’ilar suke goya wa baya tun lokacin da aka kaddamar da shi a watan Mayu.
Daga cikin mutanen dai akwai yara kanana da dama, ciki har da wani jariri dan kwana 10 da haihuwa.