HausaTv:
2025-05-27@19:39:57 GMT

 Sojojin HKI Sun Yi Wani Sabon Kisan Kiyashi A Gaza

Published: 26th, May 2025 GMT

Hare-haren sojojin HKI a yankin Gaza sun yi sanadiyyar shahadar  Falasdinawa 57

Majiyar Asibiti a yankin na Gaza,ta sanar da cewa sojojin mamayar sun kai hari ne akan makarantar ” Fahmi al-jarjawi” wacce take a yankin al-Darj’ a cikin birnin Gaza, da hakan ya yi sanadiyyar shahadar Falasdianwa 25.”

 Harin ya yi sanadiyyar konewar gawawwakin shahidan da kuma tashin gagarumar gobara a makarantar da  ‘yan hijira Falasdinawa suke ciki.

 Ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta sanar da cewa  daga 7 ga watan Oktoba 2023 zuwa yanzu adadin shahidan Falasdinawa ya haura dubu 53 da 939.

Haka  nan ma’aikatar ta ce; Wadanda su ka jikkata kuwa a wannan tsakanin sun kai dubu 122 da 797.

Sojojin HKI sun shelanta yaki ne akan yankin Gaza da zummar murkushe kungiyar Hamas, sai kuma kwato fursunonin da suke hannun ‘yan gwagwarmaya, lamarin da ya zuwa yanzu babu wanda ya tabbata.

Daga farkon yakin ne dai kungiyar Hamas ta sanar da cewa, ta hanyar tattaunawa ne kadai za a iya yin musayar fursunoni.

Ya zuwa yanzu kuwa an yi musayar fursunonin a tsakanin bangarorin biyu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gasar Wasanni Ta Kasa: Jihar Binuwai Ta Samu Kyaututtuka 9 Zuwa Yanzu

George Iniobong ɗan shekara ashirin da biyu daga tawagar Jihar Binuwai ya samu kyautar azurfa a gasar maza ta Judo mai nauyin kilo 60 a yau Lahadi, yayinda ake cigaba da gasar wasanni ta ƙasa karo na 22 (NSF) da ke gudana a Abeokuta, babban birnin jihar Ogun.

Nasarar da George ya samu ya sa tawagar ta Jihar Binuwai ta samu kyautukan tagulla da Azurfa 9 jimilla a gasar, wakilinmu ya ruwaito cewa, Iniobong, ya yi matuƙar taka rawar gani a wasan inda ya samu nasara a kan abokin karawarshi daga jihar Ogun cikin mintunan ƙarshe na karawar.

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

George Iniobong yayinda yake zantawa da manema labarai bayan samun wannan gagarumar nasarar, ya yaba wa Gwamnan Jihar Binuwai, Fr. Hyacinth Alia domin abinda ya kira gudunmawar da gwamnan ya ba shi da sauran ‘yan wasa daga jihar domin su nuna bajintarsu a wasannin na Gateway wanda ya haɗa ‘yan wasa daga dukkan jihohin kasar nan 36 da kuma babban birnin tarayya Abuja, domin fafatawa a wasanni daban-daban, da niyyar inganta hadin kai da kwazo a fadin Najeriya.

“Duk da cewar nayi tunanin samun kyautar zinare a wannan wasan amma ina sa ran kasancewa cikin masu samun wannan kyautar zuwa gaba, Nasara ta na tare dani da kuma jihar Binuwai” inji shi, “Duk da haka na ƙara samun ƙwarin gwuiwa da gogewa, kuma a shirye nake in bayar da duk abin da zan yi wajen samun nasarar jihar idan wata dama ta samu ya kara da cewa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama A Wani Sabon Hari Da Suka Kai Sansanin Sojoji A Borno
  • Sojojin Yahudawa sun Kashe Wani Matashi A Yankin Yamma Da Kogin  Jordan
  • Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Wa Yankunan Gaza Hare-hare
  • Falasdinawa 30 sun yi shahada a Wani harin Isra’ila kan wata makaranta
  • Sojojin Yamen Sun Cilla Wani Makamai Masu Linzami Kan HKI
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Wuce Gona Da Iri Kan Birnin Tul-Karam Na Falasdinu
  • ‘Yar Majalisar Dokokin Ireland Ta Yi Suka Kan Shugabannin Turai Tare Da Neman Afuwa Daga Falasdinawa
  • Gasar Wasanni Ta Kasa: Jihar Binuwai Ta Samu Kyaututtuka 9 Zuwa Yanzu
  • Afirka Ta Kudu Ta Zargi Shugaban Kasar Amurka Da  Rashin Dalili Akan Zargin Yi Wa Fararen Fatar Kasar Kisan Kiyashi