Aminiya:
2025-05-30@07:52:14 GMT

’Yar Najeriya ta tsinci miliyan 8.2 a Saudiyya ta mayar wa da mai su

Published: 29th, May 2025 GMT

Daya daga cikin maniyyata Aikin Hajjin bana daga jihar Filato mai suna Hajiya Zainab ta mayar wa da wani dan kasar Rasha kudinsa da ta tsinta a birnin Makka na kasar Saudiyya, har kimanin Naira miliyan takwas da dubu 200.

Rahotanni sun nuna matar ta tsinci guzirin maniyyacin ne a Masallacin Harami na Makka a ranar Talata .

Ta tsinci kudin ne da yawansu ya kai Dala dubu biyar, kimanin miliyan takwas da dubu 200 a Naira, idan aka canza a kan farashin N1,648 a kan kowacce Dala daya.

Babu wanda ya tayar da bam a Abuja —Wike Kotu ta yanke wa Murja Kunya hukuncin dauri a gidan yari

Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) da kuma Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Filato, Hon. Dayyabu Dauda duk sun tabbatar da faruwar lamarin.

“Ta nuna halin dattaku, gaskiya da rikon amana ta hanyar mayar da Dala dubu biyar din da ta tsinta a masallacin harami ga mai su. Hakika ta nuna halin nagarta da tausayi,” in ji Hon Dayyabu.

A wani labarin kuma, hukumar ta NAHCON ta nuna rashin jin dadinta da yadda daya daga cikin maniyyatan jihar Zamfara ta haihu a Madina a makon nan.

Hukumar ta ce ta yi mamakinn yadda matar ta tsallake duk gwaje-gwajen da ake yi a kokarin hana masu juna biyun da suka kusa haihuwa tafiya.

Sai dai ta ce za ta yi cikakken bincike domin ta gano a ina aka samu matsalar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Saudiyya

এছাড়াও পড়ুন:

An ga watan Babbar Sallah a Saudiyya

Hukumomin Kasar Saudiyya sun sanar da ganin jinjirin watan Zulhajji a ranar Talata, wanda ke nuna cewa ranar Laraba 28 ga Mayu, 2025, ita ce 1 ga watan Zulhajji, 1446 Bayan Hijira.

Hakan yana nufin Alhzai za su yi Tsayuwar Arfa ranar Alhamis, a yi Babbar Sallah ranar Juma’a na mako mai zuwaa yi

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ambaliyar Neja ta ci mutum 12 ’yan gida daya
  • NAHCON ta kammala jigilar maniyyata aikin hajjin 2025
  •  Fiye Da Falasdinawa 60 Ne Su Ka Yi Shahada A Jiya Laraba
  • DAGA LARABA: “Sai Na Tara Kudin Cin Abinci Na Nake Iya Siyan Audugar Al’ada”
  • Tinubu na neman ciyo bashin Naira tiriliyan 39 daga kasashen waje
  • Wata Hajiya ‘Yar Nijeriya Mai Shekaru 75 Ta Rasu A Saudiyya Yayin Aikin Hajji
  • An ga watan Babbar Sallah a Saudiyya
  • Yadda kotu ta yanke wa wanda ya kona mutane a cikin masallaci hukuncin rataya a Kano
  • Hukumar Kare Hakkin Bil’adam Ta MDD Ta Bukaci A Kawo Karshen Kissan Kiyashi A Gaza