Aminiya:
2025-09-18@03:30:44 GMT

Kifi jinsin Shark ya fusata ya fasa rufin gida

Published: 16th, February 2025 GMT

Wani kifi jinsin Shark da mamallakin Kamfanin Airbnb da ya shahara a duniya mai tsawon kafa 25 ya fusata, inda ya fito daga rufin gidan da yake saboda matakin da aka ɗauka na tilasta rufe gidan da aka ajiye shi.

Mamallakin Kamfanin wanda yake mazaunin Birtaniya ne, mai suna Dakta Magnus Hanson-Heine ya rasa wani shirin neman alfarma daga Karamar Hukumar Oxford na hana shi amfani da wurin zama na ɗan gajeren lokaci na cikin kadarorinsa da aka fi sani da Shark House (wato inda yake kiwon kifin).

Mazabar Tsanyawa/Kunchi ta shafe shekara guda ba tare da wakilci ba Yadda za a yaƙi talauci a Arewa maso Gabas  — Shettima

Ya yi iƙirarin cewa bai samu ƙorafi ko ɗaya daga makwabtansa ba, amma kuma hukumar yankin ta gabatar masa da korafi a kan a rufe gidan AirBnbs da ke cikin birnin.

Haka kuma, a yanzu ya buƙaci baki da su zo, su ziyarci gidan yadda za su iya, inda ya yi alkawarin ci gaba da gudanar da harkoki yadda zai iya.

Mutumin wanda mahaifin HansonHeine da Bill Heine, ya fara gina wannan gidan ba tare da izinin Karamar Hukumar Birnin Oxford a 1986 ba.

A shekaru biyar da suka gabata, ya bayar da hayar kadarorin a karkashin Kamfanin Airbnb na dan gajeren lokaci – amma ya sami sanarwa daga karamar hukumar a kan rufe gidan, bayan wani makwabcin yankin da ya koka game da canjin wurin zama zuwa wani wuri na ɗan gajeren lokaci.

Yanzu an sanar wa Hanson-Heine cewa, dole ne ya daina amfani da gidan na ɗan gajeren lokaci kafin 11 ga Maris, 2025 – matakin da ya yi imanin zai cutar da kamfaninsa dangane da yawon buɗe ido a Oxford gaba ɗaya.

“Gidan Shark babban wurin ɗaukar hankali ne na yawon buɗe ido, ba kawai kamar gidan iyali na yau da kullum ba ne.

“Abin farin ciki ne na sanar da jama’a domin su yi murna tare da mu, kuma zan ci gaba da yin hakan tsawon lokacin da zan iya,” in ji shi.

“Har yanzu ban ji wasu korafe-korafe daga makwabtanmu ba, ko da a lokacin da ake shirin daukaka ƙarar, kuma sufeton yankin bai samu wani nakasu ba a hukuncin da ya yanke,” in ji shi.

Ya ce ya samar da wannan wurin ne don yawon bude ido da yake daukar hankalin baki masu ziyartar wuraren da ya buɗe.

“Wasu daga cikin ’yan majalisar sun yi amfani da wannan a matsayin uzuri don samun wasu hujjoji na siyasa ta hanyar bin taswirar wani yanki na cikin gari don cin gajiyar jama’a,” in ji shi.

“Wannan bai ba da wani abu mai ma’ana ba, don taimaka wa mutanen da ke neman wuraren yawon buɗe ido.

“A bangaren yawon bude ido da masaukin baki yankin Oxford zai kasance mafi muni a gare shi.”

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Shark

এছাড়াও পড়ুন:

An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar

Antoni Janar na Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke birnin Yamai a Nijar, ya bayyana cewa an kama tsohon Ministan Harkokin Waje, Ibrahim Yacoubou, bisa zargin hannunsa a cikin wata aika-aika ta kisan kai domin yin tsafi.

A cewar Maazou Oumarou, lamarin ya samo asali ne daga wani binciken ’yan sanda da aka fara gudanarwa tun a ranar 29 ga Yuli, 2025.

KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja

Ya bayyana cewa, an soma gudanar da binciken ne dangane da yunƙurin kisa a wani yanki da ke wajen birnin Yamai, lamarin da ya kai ga cafke ababen zargin a garin Dosso.

Wani mutum mai suna Mahamadou Noura ne ya bayyana cewa shi ne ya yi yunƙurin kisan, tare da wasu kashe-kashe guda shida da ya aiwatar a baya, bisa umarnin wasu mutane, ciki har da tsohon ministan Ibrahim Yacoubou.

Mutumin ya shaida wa mahukunta cewa ya aikata hakan ne domin yin tsafi da gawarwakin, a madadin wasu mutane da suka haɗa da: Issa Ali Maiga da Ismael Morou Karama da Elhadji Bilya da kuma Issa Seybou Hama.

TRT ya ruwaito cewa tuni dai an cafke duk ababen zargin, yayin da Kotun Ɗaukaka Ƙarar ta umurci ’yan sanda da su ci gaba da bincike tare da ɗaukar ƙarin matakan da za su tabbatar da gaskiya.

Sanarwar ta ce: “Manufar wannan mataki na shari’a ita ce a tattara cikakken rahoto da ke ƙunshe da dukkan abubuwan da suka faru, sannan a miƙa shi ga ɓangaren gurfanarwa.”

Mai shigar da ƙara a ɓangaren gwamnati ya ce, la’akari da girman wannan lamari, wajibi ne a gudanar da bincike cikin gaggawa.

Haka kuma ya buƙaci al’umma da su mutunta ’yancin kotu tare da bayar da cikakken goyon baya domin fayyace gaskiya.

Ana iya tuna cewa, Ibrahim Yacoubou na daga cikin manyan jami’an da aka kama bayan juyin mulkin Nijar na ranar 26 ga Yuli, 2023, sai dai daga bisani an ba shi beli na wucin gadi a cikin watannin baya.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin