Aminiya:
2025-05-24@17:27:27 GMT

Kifi jinsin Shark ya fusata ya fasa rufin gida

Published: 16th, February 2025 GMT

Wani kifi jinsin Shark da mamallakin Kamfanin Airbnb da ya shahara a duniya mai tsawon kafa 25 ya fusata, inda ya fito daga rufin gidan da yake saboda matakin da aka ɗauka na tilasta rufe gidan da aka ajiye shi.

Mamallakin Kamfanin wanda yake mazaunin Birtaniya ne, mai suna Dakta Magnus Hanson-Heine ya rasa wani shirin neman alfarma daga Karamar Hukumar Oxford na hana shi amfani da wurin zama na ɗan gajeren lokaci na cikin kadarorinsa da aka fi sani da Shark House (wato inda yake kiwon kifin).

Mazabar Tsanyawa/Kunchi ta shafe shekara guda ba tare da wakilci ba Yadda za a yaƙi talauci a Arewa maso Gabas  — Shettima

Ya yi iƙirarin cewa bai samu ƙorafi ko ɗaya daga makwabtansa ba, amma kuma hukumar yankin ta gabatar masa da korafi a kan a rufe gidan AirBnbs da ke cikin birnin.

Haka kuma, a yanzu ya buƙaci baki da su zo, su ziyarci gidan yadda za su iya, inda ya yi alkawarin ci gaba da gudanar da harkoki yadda zai iya.

Mutumin wanda mahaifin HansonHeine da Bill Heine, ya fara gina wannan gidan ba tare da izinin Karamar Hukumar Birnin Oxford a 1986 ba.

A shekaru biyar da suka gabata, ya bayar da hayar kadarorin a karkashin Kamfanin Airbnb na dan gajeren lokaci – amma ya sami sanarwa daga karamar hukumar a kan rufe gidan, bayan wani makwabcin yankin da ya koka game da canjin wurin zama zuwa wani wuri na ɗan gajeren lokaci.

Yanzu an sanar wa Hanson-Heine cewa, dole ne ya daina amfani da gidan na ɗan gajeren lokaci kafin 11 ga Maris, 2025 – matakin da ya yi imanin zai cutar da kamfaninsa dangane da yawon buɗe ido a Oxford gaba ɗaya.

“Gidan Shark babban wurin ɗaukar hankali ne na yawon buɗe ido, ba kawai kamar gidan iyali na yau da kullum ba ne.

“Abin farin ciki ne na sanar da jama’a domin su yi murna tare da mu, kuma zan ci gaba da yin hakan tsawon lokacin da zan iya,” in ji shi.

“Har yanzu ban ji wasu korafe-korafe daga makwabtanmu ba, ko da a lokacin da ake shirin daukaka ƙarar, kuma sufeton yankin bai samu wani nakasu ba a hukuncin da ya yanke,” in ji shi.

Ya ce ya samar da wannan wurin ne don yawon bude ido da yake daukar hankalin baki masu ziyartar wuraren da ya buɗe.

“Wasu daga cikin ’yan majalisar sun yi amfani da wannan a matsayin uzuri don samun wasu hujjoji na siyasa ta hanyar bin taswirar wani yanki na cikin gari don cin gajiyar jama’a,” in ji shi.

“Wannan bai ba da wani abu mai ma’ana ba, don taimaka wa mutanen da ke neman wuraren yawon buɗe ido.

“A bangaren yawon bude ido da masaukin baki yankin Oxford zai kasance mafi muni a gare shi.”

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Shark

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an Sibil Difens sun bude wuta a garin Jos

Mazauna garin Jos sun shiga cikin zullumi bayan da jami’an Hukumar Tsaro ta Sibil Difens (NSCDC) suka yi ta harbe-harbe a ranar Asabar.

Jami’an na Sibil Difens da ke aiki karkashi Hukumar Kula da Ci-gaban Garin Jos (JMDB) sun bude wuta ne a yayin wani samame da suka kai katafare shagon sayar da kayayyaki na S.O Plaza, lamarin da ya haifar da rikici.

Jami’an hukumar sun kuma lakada wa wani matashi mai aiki a plazar duka, lamarin da ya rincabe zuwa tayar da jijiyoyin wuya.

A yayin samamen, jami’an tsaron sun ce sun je ne domin kama wata babbar mota da ta keta dokar  hana manyan motoci shiga garin.

Za mu gina mayankar dabbobi ta Naira biliyan 3 a Gombe —Gwamnati Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 5 a Borno

Amma wani bidiyo da ke yawo ya nuna cewa an ajiye motar ce a cikin harabar plazar kuma ba ta tare hanya ba.

Mazauna garin Jos sun bayyana cewa ba jami’an da ke aiki da JMDB sun yi kaurin suna wajen yin irin haka, inda suke lalata dukiyar jama’a a yayin samamen da suk kaiwa tare da nuna karfin makamai, da ke jefa jama’a cikin firgici.

Mamallakin S.O Plaza, Mista Solomon Okeke, the owner of S.O Plaza, ya bayyana abin a matsayin barna.

Ya kara da cewa ko a watan Agustan bara, wani Manajan Hukumar JMDB, Hart Bankat, ya jagoranci jami’an Sibil Difens zuwa plazar ya sa suka harbe tayoyi shida na wata babbar mota a cikin harabar wurin, wanda ya jawo musu asarar miliyoyin kudade.

Mista Okeke ya bayyana cewa jami’an “sun yi awon gaba da wata babbar mota cike da kaya, kuma sun yi wa wani dan shekara 19 duka suka yayyaga masa kaya, kuma har yanzu ba a san inda yak ba.

“Me ya sa duk lokacin da suka zo sai sun yi ta harbe-harbe suna dukan ma’aikata sun lalata dukiyar jama’a?”

A nasu bangaren, mazauna yakin na Bukuru sun bukaci Gwamna Caleb Mutfwang ya sanya baki tare da taka wa jami’an JMDB burki kan irin yadda suke wuce gona da iri domin a samu zaman lafiya.

Wakilinmu ya yi kokarin jin ta bakin Janar Manajan JMDB, Akitet Hart Bankat, amma har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoton haka bai samu ba, saboda jami’in bai ba da amsa ga tambayar da aka yi masa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an Sibil Difens sun bude wuta a garin Jos
  • Nijeriya Na Da Karfin Tattalin Arzikin Sarrafa Kayan Dandanon Da Muke Bukata A Cikin Gida – Yahaya Yakubu
  • SojojinHKI Sun Kashe Akalla Mutane 75 A Gaza A Ranar Jumma’a Kadai
  • Sin Da ASEAN Sun Kammala Tattaunawa Game Da Kafa Yankin Ciniki Cikin ‘Yanci
  • Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
  • ‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu
  • Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Amurka Ya Bukaci Amurka Ta Jefa Makaman Nukliya Kan Gaza
  • Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin
  • An kama wani matashi da ya yi shigar mata a Adamawa
  • Iran Ta Gamsu Da Lokaci Da Wurin Da Za A Gudanar Da Shawarwarinta Da Amurka Zagaye Na Biyar