Kifi jinsin Shark ya fusata ya fasa rufin gida
Published: 16th, February 2025 GMT
Wani kifi jinsin Shark da mamallakin Kamfanin Airbnb da ya shahara a duniya mai tsawon kafa 25 ya fusata, inda ya fito daga rufin gidan da yake saboda matakin da aka ɗauka na tilasta rufe gidan da aka ajiye shi.
Mamallakin Kamfanin wanda yake mazaunin Birtaniya ne, mai suna Dakta Magnus Hanson-Heine ya rasa wani shirin neman alfarma daga Karamar Hukumar Oxford na hana shi amfani da wurin zama na ɗan gajeren lokaci na cikin kadarorinsa da aka fi sani da Shark House (wato inda yake kiwon kifin).
Ya yi iƙirarin cewa bai samu ƙorafi ko ɗaya daga makwabtansa ba, amma kuma hukumar yankin ta gabatar masa da korafi a kan a rufe gidan AirBnbs da ke cikin birnin.
Haka kuma, a yanzu ya buƙaci baki da su zo, su ziyarci gidan yadda za su iya, inda ya yi alkawarin ci gaba da gudanar da harkoki yadda zai iya.
Mutumin wanda mahaifin HansonHeine da Bill Heine, ya fara gina wannan gidan ba tare da izinin Karamar Hukumar Birnin Oxford a 1986 ba.
A shekaru biyar da suka gabata, ya bayar da hayar kadarorin a karkashin Kamfanin Airbnb na dan gajeren lokaci – amma ya sami sanarwa daga karamar hukumar a kan rufe gidan, bayan wani makwabcin yankin da ya koka game da canjin wurin zama zuwa wani wuri na ɗan gajeren lokaci.
Yanzu an sanar wa Hanson-Heine cewa, dole ne ya daina amfani da gidan na ɗan gajeren lokaci kafin 11 ga Maris, 2025 – matakin da ya yi imanin zai cutar da kamfaninsa dangane da yawon buɗe ido a Oxford gaba ɗaya.
“Gidan Shark babban wurin ɗaukar hankali ne na yawon buɗe ido, ba kawai kamar gidan iyali na yau da kullum ba ne.
“Abin farin ciki ne na sanar da jama’a domin su yi murna tare da mu, kuma zan ci gaba da yin hakan tsawon lokacin da zan iya,” in ji shi.
“Har yanzu ban ji wasu korafe-korafe daga makwabtanmu ba, ko da a lokacin da ake shirin daukaka ƙarar, kuma sufeton yankin bai samu wani nakasu ba a hukuncin da ya yanke,” in ji shi.
Ya ce ya samar da wannan wurin ne don yawon bude ido da yake daukar hankalin baki masu ziyartar wuraren da ya buɗe.
“Wasu daga cikin ’yan majalisar sun yi amfani da wannan a matsayin uzuri don samun wasu hujjoji na siyasa ta hanyar bin taswirar wani yanki na cikin gari don cin gajiyar jama’a,” in ji shi.
“Wannan bai ba da wani abu mai ma’ana ba, don taimaka wa mutanen da ke neman wuraren yawon buɗe ido.
“A bangaren yawon bude ido da masaukin baki yankin Oxford zai kasance mafi muni a gare shi.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Shark
এছাড়াও পড়ুন:
An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo
“Saurayin nata ne ya kashe marigayiyar a ranar Talata kuma ya kulle ta a cikin dakinsa, maƙwabta ne suka ja hankalin daliban a lokacin da suka fahimci wani wari daga dakin.
“Har yanzu ba mu san dalilin da ya sa saurayin ya kashe ta ba, dalibar tana sana’ar POS a yankin, amma tun ranar Talata, ta ɓace kuma babu wanda ya san inda take sai jiya, lokacin da maƙwabta suka ji wani wari daga dakin saurayinta.
“Shi yaron, bayan sun kashe ta, ya tafi da cinikin da yi a wajen sana’ar ta ta POS.
“Lokaci ya yi da gwamnatin jihar za ta yi wani abu game da kashe-kashen da ƴan asalin garin suke yi wa dalibanmu, idan ba a yi wani abu ba, hakan na iya haifar da mummunan rikici a wannan al’umma.
“Idan za ku iya tunawa a makonnin da suka gabata, an kuma sace dalibanmu biyu tare da kashe su, don haka dole a yi wani abu.”
A halin da ake ciki, daliban, a yayin zanga-zangar, sun rera waƙoƙin haɗin kai daban-daban, dauke da kwalaye da rubuce-rubuce irin su, ‘A Akungba Akoko, ka ce kada a kashe dalibai’, ‘A daina kashe mu, daliban AAUA,’ ƴa kamata gwamnatin jihar ta sa baki wajen kashe daliban AAUA,’ da dai sauransu.
da take mayar da martani game da sabon kashe-kashen da aka yi a cikin al’ummar jami’ar, kwamitin haɗin gwiwa na ƙungiyar daliban Nijeriya ta ƙasa, ta yi Allah-wadai da wannan danyen aikin tare da yin kira ga jami’an tsaro da su gurfanar da wanda ya aikata laifin.
“ƙungiyar daliban Nijeriya ta ƙasa, Joint Campus Council, Ondo Aɗis ta yi matuƙar kaɗuwa tare da nuna alhinin ta dangane da yawaitar kashe-kashen da ake yi wa daliban Jami’ar Adekunle Ajasin, Akungba Akoko, Jihar Ondo.
Tuntubi kakakin rundunar ƴansandan jihar, Ayanlade Olayinka, ya tabbatar da kisan.
Ayanlade ya ce saurayin marigayin ya gudu daga cikin al’umma kuma nan ba da jimawa ba jami’an ƴansanda za su kamo shi.
Ya ce an kama mutane uku da ake zargin ana yi musu tambayoyi kan kisan da aka yi a jami’ar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp