Shekaru 6: Don amfanin matasa mun inganta harkokin ilimi, noma — Gwamna Buni
Published: 30th, May 2025 GMT
A bikin cikarsa shekaru 6 cur yana mulkin Jihar Yobe, Gwamnan jihar Mai Mala Buni da aka gudanar a ranar Alhamis ɗin da ta gabata ya bayyana irin gagarumin ci gaban da aka samu akan harkokin ilimi da noma, inda ya ce akasarin waɗanda suka amfana a waɗannan fannoni guda biyu matasa ne.
Da yake jawabi a yayin wannan taro na bikin cikarsa shekaru 6 akan mulki da aka gudanar a babban ɗakin taro na Banquet da ke gidan gwamnatin Jihar a garin Damaturu tare da ma su ruwa da tsaki na Jihar.
Gwamnan ya bayyana ƙudirinsa na ci gaba da inganta harkokin da suka shafi matasa da kuma sauran fannonin da tuni gwamnatinsa ta yi nisa cikinsu kamar fannonin noma, kiwon lafiya, kasuwanci, tsaro da makamantansu.
Taron wanda ofishin mai baiwa Gwamna shawara na musamman kan harkokin talabijin, Rediyo da kafafen yaɗa labarai na zamani, Dakta Ibrahim Yabani, ya shirya yadda gwamnan ya amsa tambayoyin da wasu al’ummomin Jihar haɗe da ‘yan jaridu da ƙungiyoyin farar hula daga ƙananan hukumomin Jihar 17 suka yi wanda nan take Gwamnan ke amsa musu tambayoyin da suka masa kai tsaye.
A nasa jawabin, Gwamna Buni ya jaddada cewa taimakawa matasa na da matuƙar muhimmanci wanda kamar yadda ya ambata hakan ne ya ba shi ƙarfin gwiwar ƙara inganta harkokin ilimi wanda matuƙar matasa sun samu Ilimi to kuwa batun zaman banza zai kau kasancewar da sun samu Ilimi mai amfani gwamnatin nada ƙarfin gwiwar samar musu da aikin yi ta kowace irin fuska.
Gwamnan ya ce, aƙalla gwamnatin Jihar a duk wata takan kashe zunzurutun kuɗi sama da Naira miliyan 600 wajen ciyar da ɗaliban makarantun kwana waɗanda dukkansu matasa ne kuma gwamnatinsa ta tura matasa sama da 100 zuwa ƙasar Indiya don samun horo akan karantun likita wanda a yanzu haka matasan sun kammala sun dawo Jihar har an samar musu aikin yi a asibitocin Jihar.
Kan ɓangaren noma ma haka lamarin yake domin gwamnatinsa ta samarwa matasan kayayyakin gudanar da noman zamani, wadda kuma kwalliya tuni ta biya kuɗin sabulu.
Haka nan ta ɓangare tsaro nan ma haka lamarin yake domin gwamnatin ta a kullum takan yi abin da ya dace dangane da harkokin na tsaro musamman ta wajen samarwa jami’an tsaron Jihar haɗe da na Sibilyan JTF kayan aikin da suka haɗa da motocin sintiri da sauransu don ganin an daƙile barazanar da masu tada ƙayar baya ke yi ga al’ummar Jihar.
Ta fuskar gina titunan karkara ma gwamnatinsa ba ta yi ƙasa a gwiwa ba kasancewar yana da matuƙar muhimmanci wajen harkokin inganta kasuwanci, aikin noma haɗa kan al’umma musamman a ƙananan hukumomin Potiskum da Damaturu da Nguru da Gashua da Geidam da aka gina musu hanyoyin mota don ƙara alatu a garuruwan da kuma gina hanyoyin karkara a ƙananan hukumomin Jihar.
Da yake amsa tambayoyi daga mahalarta taron, Buni ya bayyana cewa, yawan gina hanyoyin mota ba wai rage tsadar sufuri ba ne, har ma yana ƙara haɓaka tattalin arzikin yankunan gaba ɗaya ta hanyar sauƙaƙawa manoman kawo amfanin gonakinsu zuwa kasuwannin Jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamna Buni Gwamnan Jihar Yobe harkokin ilimi da noma
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
Daga Usman Muhammad Zaria
Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.
Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.
Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.
Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.
Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen tsaro.
CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.