Aminiya:
2025-07-25@00:07:25 GMT

Sojoji sun halaka mayakan ISWAP da dama a Borno

Published: 28th, May 2025 GMT

Dakarun sojojin Najeriya sun dakile wani harin hadin gwiwa da ‘yan ta’addar Boko Haram da ISWAP suka kai a yankin Marte da ke jihar Borno, inda suka kashe wasu da dama daga cikin maharan.

Majiyar leken asirin hedikwatar sojan Najeriya ta tabbatar  da cewa harin ya faru ne da misalin karfe 1:35 na wayewar safiyar talata 27 ga watan Mayu.

Majiyar ta ce wasu ’yan ta’adda da ba a tabbatar da adadin su ba sun kai hari a bataliya ta 50 da ke Marte.

Kotu ta ci su El-Rufa’i tarar miliyan 900 Tinubu ya ɗaga darajar Kwalejin Kimiyya  ta Kabo Zuwa Jami’ar Fasaha ta Tarayya

Dakarun da ke samun goyon bayan wata tawaga ta runduna ta 24 da bataliya ta musamman ta 134, sun yi gaggawar fafatawa da ’yan ta’addan a wani kazamin fadan da aka kwafsa.

A cewar rahoton, dakarun rundunar sojojin saman Najeriya na Operation Hadin Kai, ta aiwatar da aikin leken asiri ta sama, da kuma dauki ba dadi, wanda ya taka rawar gani wajen fatattakar ’yan tada kayar bayan da suka tsere.

Majiyar ta ce sojojin sun yi nasarar dakile harin tare da dawo da cikakken iko a yankin, yayin da ake ci gaba da gudanar da aikin zakulo abubuwan da suka rage da kuma kwato makamai da kayan aikin da ’yan ta’addan ke amfani da su.

“Sojoji biyu sun rasa ransu a yayin wannan farmaki, sannan an samu wasu asarorin kayayyakin da suka hada da lalacewar wata babbar mota mai dauke da bindiga da kuma tayar wata motar sojoji,” in ji majiyar.

Harin na baya-bayan nan a Marte na zuwa ne a daidai lokacin da sojoji ke dada kai hare-hare a yankin tafkin Chadi da arewacin Borno, inda kungiyoyin ISWAP da Boko Haram suka yi yunkurin sake kafa sansanoninsu.

A halin da ake ciki dai, ana ci gaba da sanya ido sosai kan harkokin tsaro a jihar Borno, inda ake ci gaba da gudanar da sintiri da tattara bayanan sirri da nufin hana kutse a nan gaba, in ji majiyar ta sojan Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram Marte

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Cututtukan da rumar daki ke haifarwa ga jikin mutum

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Masana kiwon lafiya sun bayyana yadda ruma ke yada matsalolin rashin lafiya ga lafiyar jikin mutum.

Musamman a lokuta irin na damina, ruma kan dabaibaye gidajen mutane da dama na tsawon lokaci wanda ka iya jawo matsaloli daban-daban ga lafiya da kuma gidajenmu.

NAJERIYA A YAU: Yadda tsadar taki ke hana noman masara da shinkafa DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan irin matsalolin da ruma ke haifarwa ga lafiyar jikin namu.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamantin Kasar Siriya Ta Rufe Hanyoyin Shiga BirninSiweida Na Kasar Saboda Ci Gaba Da Bullar Rikici
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 95 a Neja, sun ceto mutum 138 da aka sace
  • Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid a Borno
  • NAJERIYA A YAU: Cututtukan da rumar daki ke haifarwa ga jikin mutum
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid A Borno
  • Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa Sun Gamsu Zuba Jari A Sin Dama Ce Ta Cimma Nasarar More Riba A Nan Gaba
  • HOTUNA: An ƙaddamar da aikin sabunta ginin Majalisar Dokokin Bauchi
  • Sin Ta Samar Da Karin Guraben Aikin Yi Miliyan 6.95 A Rabin Farko Na Bana
  • Asibitin ATBUTH za ta fara gwajin rigakafin zazzaɓin Lassa
  • NAJERIYA A YAU: Yadda tsadar taki ke hana noman masara da shinkafa