Aminiya:
2025-11-02@21:11:35 GMT

Sojoji sun halaka mayakan ISWAP da dama a Borno

Published: 28th, May 2025 GMT

Dakarun sojojin Najeriya sun dakile wani harin hadin gwiwa da ‘yan ta’addar Boko Haram da ISWAP suka kai a yankin Marte da ke jihar Borno, inda suka kashe wasu da dama daga cikin maharan.

Majiyar leken asirin hedikwatar sojan Najeriya ta tabbatar  da cewa harin ya faru ne da misalin karfe 1:35 na wayewar safiyar talata 27 ga watan Mayu.

Majiyar ta ce wasu ’yan ta’adda da ba a tabbatar da adadin su ba sun kai hari a bataliya ta 50 da ke Marte.

Kotu ta ci su El-Rufa’i tarar miliyan 900 Tinubu ya ɗaga darajar Kwalejin Kimiyya  ta Kabo Zuwa Jami’ar Fasaha ta Tarayya

Dakarun da ke samun goyon bayan wata tawaga ta runduna ta 24 da bataliya ta musamman ta 134, sun yi gaggawar fafatawa da ’yan ta’addan a wani kazamin fadan da aka kwafsa.

A cewar rahoton, dakarun rundunar sojojin saman Najeriya na Operation Hadin Kai, ta aiwatar da aikin leken asiri ta sama, da kuma dauki ba dadi, wanda ya taka rawar gani wajen fatattakar ’yan tada kayar bayan da suka tsere.

Majiyar ta ce sojojin sun yi nasarar dakile harin tare da dawo da cikakken iko a yankin, yayin da ake ci gaba da gudanar da aikin zakulo abubuwan da suka rage da kuma kwato makamai da kayan aikin da ’yan ta’addan ke amfani da su.

“Sojoji biyu sun rasa ransu a yayin wannan farmaki, sannan an samu wasu asarorin kayayyakin da suka hada da lalacewar wata babbar mota mai dauke da bindiga da kuma tayar wata motar sojoji,” in ji majiyar.

Harin na baya-bayan nan a Marte na zuwa ne a daidai lokacin da sojoji ke dada kai hare-hare a yankin tafkin Chadi da arewacin Borno, inda kungiyoyin ISWAP da Boko Haram suka yi yunkurin sake kafa sansanoninsu.

A halin da ake ciki dai, ana ci gaba da sanya ido sosai kan harkokin tsaro a jihar Borno, inda ake ci gaba da gudanar da sintiri da tattara bayanan sirri da nufin hana kutse a nan gaba, in ji majiyar ta sojan Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram Marte

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi

 

Shugaba Xi ya kuma bayyana cewa, cikakken zama na 4 na kwamiti na 20 na JKS ya amince da shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15. Sin za ta yi amfani da wannan damar don ci gaba da gyare-gyaren tattalin arzikinta, da kuma fadada bude kasuwancinta mai zurfi ga ketare, ta haka za ta ci gaba da ba da sabbin damammaki ga yankin Asiya da Pasifik da sauran kasashen duniya ta hanyar zamanantar da al’ummarta. (Amina Xu)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo October 30, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma  October 30, 2025 Daga Birnin Sin Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Duk Wani Kutse Na Isra’ila A Kudancin Kasar
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari