Aminiya:
2025-09-17@23:11:16 GMT

Sojoji sun halaka mayakan ISWAP da dama a Borno

Published: 28th, May 2025 GMT

Dakarun sojojin Najeriya sun dakile wani harin hadin gwiwa da ‘yan ta’addar Boko Haram da ISWAP suka kai a yankin Marte da ke jihar Borno, inda suka kashe wasu da dama daga cikin maharan.

Majiyar leken asirin hedikwatar sojan Najeriya ta tabbatar  da cewa harin ya faru ne da misalin karfe 1:35 na wayewar safiyar talata 27 ga watan Mayu.

Majiyar ta ce wasu ’yan ta’adda da ba a tabbatar da adadin su ba sun kai hari a bataliya ta 50 da ke Marte.

Kotu ta ci su El-Rufa’i tarar miliyan 900 Tinubu ya ɗaga darajar Kwalejin Kimiyya  ta Kabo Zuwa Jami’ar Fasaha ta Tarayya

Dakarun da ke samun goyon bayan wata tawaga ta runduna ta 24 da bataliya ta musamman ta 134, sun yi gaggawar fafatawa da ’yan ta’addan a wani kazamin fadan da aka kwafsa.

A cewar rahoton, dakarun rundunar sojojin saman Najeriya na Operation Hadin Kai, ta aiwatar da aikin leken asiri ta sama, da kuma dauki ba dadi, wanda ya taka rawar gani wajen fatattakar ’yan tada kayar bayan da suka tsere.

Majiyar ta ce sojojin sun yi nasarar dakile harin tare da dawo da cikakken iko a yankin, yayin da ake ci gaba da gudanar da aikin zakulo abubuwan da suka rage da kuma kwato makamai da kayan aikin da ’yan ta’addan ke amfani da su.

“Sojoji biyu sun rasa ransu a yayin wannan farmaki, sannan an samu wasu asarorin kayayyakin da suka hada da lalacewar wata babbar mota mai dauke da bindiga da kuma tayar wata motar sojoji,” in ji majiyar.

Harin na baya-bayan nan a Marte na zuwa ne a daidai lokacin da sojoji ke dada kai hare-hare a yankin tafkin Chadi da arewacin Borno, inda kungiyoyin ISWAP da Boko Haram suka yi yunkurin sake kafa sansanoninsu.

A halin da ake ciki dai, ana ci gaba da sanya ido sosai kan harkokin tsaro a jihar Borno, inda ake ci gaba da gudanar da sintiri da tattara bayanan sirri da nufin hana kutse a nan gaba, in ji majiyar ta sojan Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram Marte

এছাড়াও পড়ুন:

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar Sin ya gudanar da taron manema labarai da misalin karfe 10 na safiyar yau Litinin, inda kakakin hukumar kididdiga ta kasar, kuma babban masanin tattalin arziki, kana daraktan sashen kididdigar tattalin arziki na kasar, Fu Linghui ya yi karin haske kan ayyukan tattalin arzikin kasar cikin watan Agustan bana, tare da amsa tambayoyin manema labarai.

A cewar bayanan da aka gabatar a yayin taron, ayyukan tattalin arzikin kasar a watan Agusta sun samu ci gaba ba tare da tangarda ba. Kuma hakan ya bayyana ne ta hanyoyi daban-daban kamar haka: masana’antu sun habaka cikin sauri, masana’antar kera kayayyakin aiki da masana’antar fasaha sun samu ci gaba mai kyau. Kana ayyukan bayar da hidima su ma sun bunkasa cikin sauri. Baya ga haka, an samu ci gaba mai kyau a bangaren bayar da hidimomi na zamani. Harkokin kasuwanci sun samu ci gaba cikin natsuwa, inda harkokin sayar da kayayyaki ga masu sayayya suka kara habaka. Har ila yau, kadarorin jari sun ci gaba da karuwa, jarin masana’antu ya habaka cikin sauri, harkokin fice da shigen kayayyaki sun ci gaba da girma, tsarin kasuwanci ya ci gaba da ingantuwa, kana yanayin samar da guraben aikin yi, ya kasance kan wani mataki mai daidaito. Sai dai kuma saboda yanayin da ake ciki, adadin marasa aikin yi a birane ya karu, ma’aunin Core CPI ya ci gaba da hauhawa, kana faduwar farashin kayayyakin masana’antu ya ragu.

Bayanan sun kara da cewa, akwai bukatar lura da cewa, ana fuskantar yanayin rashin tabbas a waje, kuma tattalin arzikin kasar Sin yana fuskantar kalubale da hadari da yawa. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa