Leadership News Hausa:
2025-07-12@00:38:56 GMT

Babu Wasu Masu Juya Tinubu Ta Bayan Fage Ministan Yaɗa Labarai

Published: 26th, May 2025 GMT

Babu Wasu Masu Juya Tinubu Ta Bayan Fage Ministan Yaɗa Labarai

Ya ce: “Ya kamata ku nazarci Shugaban Ƙasa sosai. Za ku iya faɗin ra’ayoyin ku; zai saurare ku, amma a ƙarshe shawarar da zai yanke tasa ce. Ina ganin ya dace mu gane hakan.”

 

Yayin da yake bayani kan taken taron, ministan ya ce Shugaba Tinubu na da cikakkiyar niyya wajen aiwatar da Shirin Sabunta Fata — wanda tsari ne da ya mayar da hankali kan jin daɗin talaka da fitar da cikakken ƙarfin Nijeriya.

 

“Shirin Sabunta Fata na da nufin kawo sauyi mai ma’ana ga rayuwar al’ummar Nijeriya ta hanyar muhimman matakai da za su fitar da cikakken ƙarfin Nijeriya, ta hanyar da ba a taɓa gani ba,” inji ministan.

 

Idris ya bayyana cewa Shugaba Tinubu ya karɓi mulki ne a lokacin da Nijeriya take cikin mawuyacin hali, amma ya ɗauki matakai da gaggawa tun daga farko.

 

Ya ce: “Daga cikin abubuwan farko da Shugaban Ƙasa ya aikata su ne aiwatar da cire tallafin mai da cire tallafin musayar kuɗi, waɗanda suka daɗe suna hana cigaban Nijeriya, suna haifar da asarar biliyoyin daloli a duk shekara.”

 

Ya ƙara da cewa sakamakon waɗannan sauye-sauyen yanzu ya fara bayyana a fannoni da dama kamar ababen more rayuwa, harkar ma’adinai da ta man fetur.

 

“A matakin tarayya, ƙarin kuɗaɗen shiga sun buɗe ƙofofi ga manyan ayyukan ababen more rayuwa,” inji shi.

 

Ya lissafa wasu manyan hanyoyi guda huɗu — hanyar Legas zuwa Kalaba, da hanyar Sakkwato zuwa Badagiri, da hanyar Kalaba zuwa Abuja da hanyar Akwanga-Jos-Bauchi-Gombe — waɗanda suka haura kilomita 2,600.

 

Ya kuma ambaci aikin layin dogo na Kano zuwa Kaduna a matsayin muhimmin tsari a ƙarƙashin Shirin Sabunta Fata da kuma sashe mai muhimmanci na shirin layin dogo daga Legas zuwa Kano.

 

A ɓangaren gidaje, ya ce an ƙaddamar da ayyukan Birane da Gidajen Shirin Sabunta Fata domin rage giɓin gidaje a ƙasa, da ƙirƙirar ayyukan yi da farfaɗo da birane.

 

Don tallafa wa bunƙasar tattalin arziki na zamani, Idris ya ce Gwamnatin Tarayya na shimfiɗa wayoyin intanet har kilomita 90,000 a faɗin ƙasar nan.

 

Ya bayyana wannan yunƙuri da cewa, “matakin shimfiɗar ‘broadband’ da ba a taɓa yi ba zai rufe giɓin intanet a ƙasa, ya tallafa wa mulkin zamani, ya jawo jari na fasaha, da kuma bai wa sassa kamar ilimi, lafiya da kasuwanci damar amfani da sana’o’in intanet.”

 

Ya bayyana cewa sama da ɗalibai 300,000 ke amfana da Asusun Rancen Ilimi na Ƙasa (NELFUND), sannan ma’aikata na amfani da sabon Tsarin Lamunin Kayayyaki domin sayen muhimman abubuwan buƙata.

 

A fannin tsaro, Ministan ya ce: “Sojojin mu sun kashe dubban ‘yan ta’adda tare da ceto kusan mutane 10,000. An samu sababbin jiragen sama fiye da 25, yayin da Rundunar Sojan Ruwa ta karɓi sababbin jiragen ruwa guda huɗu.”

 

Ya yaba wa Shugaban Ƙasa bisa kafa Ma’aikatar Raya Kiwo da kuma kafa Hukumomin Raya Yankuna a kowane yanki shida na ƙasar, domin farfaɗo da noma da tabbatar da cigaban da ya shafi kowane yanki.

 

Ministan ya jaddada cewa Shirin Sabunta Fata tsari ne mai cike da kulawa ga rayuwar al’umma.

 

Ya ce: “A ƙarshen kowane shiri da manufofin gwamnatin Tinubu akwai ɗan Nijeriya talaka wanda rayuwar sa ke samun sauyi mai kyau. Ɗan Nijeriya da ke samun damar samun kuɗi don kan sa ko kasuwanci; ɗan Nijeriya da ke ganin farashin abinci yana sauka; ɗan Nijeriya da ke amfani da hanyoyin sufuri masu arha ta hanyar iskar gas ta CNG; ɗan Nijeriya da ke samun wutar lantarki ta hanyar ɗaya daga cikin shirye-shiryen wutar lantarki na gwamnati; ɗan Nijeriya da ɗan sa ko ‘yar sa ke samun damar zuwa jami’a ta hanyar NELFUND.”

 

Idris ya kuma ambaci manufar ‘Renewed Hope Nigeria First’ da aka zartar kwanan nan wadda ke wajabta wa dukkan ma’aikatun gwamnati su fifita amfani da kayan Nijeriya da ayyuka da ƙwarewar ‘yan ƙasa wajen kashe kuɗin gwamnati.

 

Ya ce: “Wannan abin tarihi ne da ba a taɓa samun irin sa ba, da burin ƙarfafa masana’antu ta hanyar samar da kaya a gida da kuma kare tattalin arzikin Nijeriya daga girgizar da ke faruwa a duniya.

 

“Shugaban mu, muna maka godiya da samun wannan tsari na kishin ƙasa, da kuma ginin tubalin farfaɗo da tattalin arzikin Nijeriya.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: ɗan Nijeriya da Nijeriya da ke

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

Amurka ta bayyana dalilin sabunta manufofin, tare da lura da cewa “an tsara sharuddan bizar Amurka da ka’idoji domin kare tsarin shige da fice na Amurka.”

Ofishin jakadancin ya kara da cewa “wadannan ka’idoji sun dogara ne kan ma’aunin fasaha da tsaro na duniya.”

A cewar ofishin jakadancin Amurka yana aiki tare da hukumomin Nijeriya domin cimma wadannan matakan.

Sanarwar ta ce “Tawagar Amurka tana aiki tare da gwamnatin Nijeriya domin tabbatar da cewa Nijeriya za ta iya cika sharuddan.”

Misalin wannan sabon tsari ya hada da “Takardun tafiye-tafiye masu aminci: tabbatar da cewa kasashe suna ba da amintattun takaddun balaguro tare da ingantattun bayanan matafiyi, Kada aikin gudanar da Bisa ya wuce lokacin da aka dauka:.”

Duk da sabbin takunkumin, ofishin jakadancin ya sake jaddada alakar diflomasiyya da Nijeriya.

Sanarwar ta kara da cewa, “Amurka na mutunta dangantakarta da Nijeriya da dadewa, kuma tana ci gaba da jajircewa wajen fadada hadin gwiwarmu bisa mutunta juna, da muhimman batutuwan tsaro, da damar tattalin arziki, tare da tabbatar da tsaron kasashen biyu.”

Har ila yau, ofishin jakadancin ya nuna goyon bayansa ga sauye-sauyen da Nijeriya ke ci gaba da yi, inda ta ce, “Mun yaba da kokarin da hukumomin shige da fice da na tsaro na gwamnatin Nijeriya ke yi na ganin sun cika ka’idoji kyawawan ayyuka na kasa da kasa.”

An shawarci matafiya na Nijeriya da su bi ka’idojin bizar.

“An bukaci matafiya ‘yan Nijeriya da su mutunta tare da kiyaye sharuddan bizarsu, kuma su tabbatar da ingantattun takaddun balaguro, kuma na zamani.”

Ofishin jakadancin ya karkare da jaddada huldarsa da jama’a da gwamnatin Nijeriya.

“Amurka ta kasance amintacciya a cikin zurfafa dangantakar jama’a da Nijeriya ta hanyar kasuwanci, ilimi da mu’amalar al’adu.

“Muna fatan ci gaba da hadin gwiwa a dukkan matakai tare da jama’ar Nijeriya da jami’an gwamnati don tabbatar da tafiya cikin aminci da doka tsakanin Amurka da dukkan kasashe,” in ji ta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku
  • Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista
  • Mayakan Huthi Sun Kara Kai Wasu Hare-Hare da Makamai Masu Linzami Kan BenGurio
  • EFCC Ta Yi Gargadi Kan Damfara Ta Hanyar Kuɗaɗen Intanet da Zuba Jari
  • Sojoji sun tarwatsa matsugunin ’yan ta’adda da kashe wasu a Borno
  • Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista
  • Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista
  • UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba
  • Sojojin Yemen Sun Nutsar Da Jirgin Ruwan “Eternity” Dake Hanyar Zuwa HKI
  • Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC