Yadda kotu ta yanke wa wanda ya kona mutane a cikin masallaci hukuncin rataya a Kano
Published: 27th, May 2025 GMT
Babbar Kotun Musulunci a Jihar Kano ta yanke wa Shafiu Abubakar hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda cinna wuta a wani masallaci a kauyen Gadan, Karamar Hukumar Gezawa, yayin da jama’a ke tsaka da jam’in sallar asuba a ranar 15 ga Mayu, 2024. Harin ya yi sanadiyar mutuwar mutane 23 tare da raunana wasu.
An samu Shafi’u da laifuka hudu, ciki har da kisan kai da kuma barna ta hanyar gobara. Baya ga hukuncin kisa, alkali ya ba da umarnin a yi masa bulala 150, tare da biya tarar N1,500, sannan kuma a kwace babur dinsa mai kafa uku, inda za a sayar, a yi amfani da kudin da aka samu wajen gyaran masallacin da ya lalace.
Yayin shari’ar, masu gabatar da kara sun gabatar da shaidu bakwai, ciki har da hakimin kauye da kuma wani jami’in ’yan sanda.
Daya daga cikin shaidun, wanda dan uwan Shafi’u ne, ya bayyana cewa wanda ake tuhumar yana da tarihin kokarin cutar da ’yan uwa, kuma an bayyana shi a matsayin mai cikakken hankali bayan binciken tabin hankali.
An yanke wa wanda ya yi wa agolarsa fyaɗe ɗaurin rai-da-rai Jama’ar gari sun kashe DPO, sun ƙona ofishin ’yan sanda a KanoWani shaida kuma ya bayyana yadda ya tsira a lokacin da masallacin da ke ci da wuta tare da munanan raunuka kuma ya ga Shafi’u yana gudu.
Shafiu ya shaida wa kotun cewa ya sayi man fetur a ranar 14 ga Mayu, 2024, don yayyafa wa masallacin sannan ya cinna masa wuta, ya rufe kofofinsa kuma ya samu konewa a lokacin da yake aikata laifin. Furucinsa, tare da konewar da ke bayyane a hannayensa yayin bayyanarsa a kotu, sun tabbatar da shari’ar masu gabatar da kara.
Daraktan gabatar da kara na Jihar Kano ya bayyana gamsuwarsa da hukuncin, inda ya bayyana cewa ya nuna girman laifin.
Sai dai lauyan Shafi’u ya nuna yiwuwar daukaka kara tare da nuna damuwa game da yanayin da yake tsare.
An ruwaito cewa lamarin ya samo asali ne daga rikicin gado, inda Shafi’u ya yi niyyar kai hari ga ’yan uwansa da ya yi imanin sun zalunce shi.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
Fitattun dalibai akalla 12 ne daga makarantun gwamnati suka samu guraben tallafin karatun sakandare a ƙarƙashin Asusun Tallafin Karatu na Jihar Kwara (Kwara-ETF).
A wajen taron gabatarwa ga waɗanda suka fara cin moriyar shirin, Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya bayyana cewa ci gaban harkar ilimi a Najeriya abu ne mai tsada kuma ya zama wajibi kowa ya bayar da gudummawarsa.
Ya roƙi masu masu hannu da shuni da kungiyoyi masu zaman kansu da su tallafa wajen gina makarantu ko kuma su ɗauki nauyin daliban da suka nuna bajinta da jajircewa a harkar karatu.
A cewarsa, an zabo daliban 12 ne sakamakon bajintar da suka nuna a matakai daban-daban na tantancewa da Kwara ETF ta gudanar.
Gwamnan ya bayyana cewa tallafin ya kunshi dukkan kuɗin da ake buƙata a karatun sakandaren daliban.
“Muna kira da jama’a su ba da gudummawa da kuma ɗaukar nauyin ɗalibai. Kada a bar wannan aiki ga gwamnati da iyaye kadai. Ilimantar da ‘ya’yanmu hakki ne da ya rataya a kanmu gaba ɗaya,” in ji Gwamna.
Ya yaba da tsarin zaɓen kuma ya taya waɗanda suka yi nasara murna.
A nata jawabin, Babbar Shugabar Kwara ETF, Oluwadamilola Amolegbe, ta ce daliban 12 sun fito ne daga cikin jerin ɗalibai 640 da aka fara tantancewa bisa cancanta.
Ta bayyana cewa tsarin zaɓen ya fara ne da rubuta jarabawa ga dukkan daliban firamare na aji shida da suka amfana da shirin KwaraLEARN na koyon fasahar zamani, har zuwa lokacin da aka kammala tantancewa.
Ali Muhammad Rabi’u