Aminiya:
2025-07-12@11:10:13 GMT

Gwamnatin Kano za ta sabunta masallacin da aka kona masallata 23 a kan N150m

Published: 27th, May 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kashe Naira miliyan dari da hamsin da ɗaya da dubu dari takwas da sittin da uku (N151,863,895.97) domin sake gina wani masallaci da wani matashi ya cinna wa wuta a yayin da jama’a ke tsaka da sallar Asuba a cikin jam’i a Tiga Gadan da ke Karamar Hukumar Gezawa, a watan Mayun bara.

Aikin sabunta masallacin ya kunshi gina makarantar Islamiyya tare da ofis da bandaki da kuma rijiyar burtsatse mai amfani da hasken rana tare da tankin ruwa na sama.

Kwamishinan Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kano, Ibrahim Abdullahi Wayya, ya sanar amincewar sake gina masallacin ya biyo bayan alkawarin da Gwamna Abba Kabir ya yi a lokacin da ya ziyarci wurin da abin ya faru.

Ya yi kira ga mutanen kauyen Gadan da su saka wannan karimci ta hanyar bayar da goyon bayan da ake bukata don tabbatar da nasarar kammala aikin, da kuma samar da kariya ga sabbin gine-ginen.

Yadda kotu ta yanke wa wanda ya kona mutane a cikin masallaci hukuncin rataya a Kano Amarya ta kashe uwargida da wuka a Katsina An yanke wa wanda ya yi wa agolarsa fyaɗe ɗaurin rai-da-rai 

A ranar Litinin ne Babbar Kotun Musukunci ta yanke wa Shafi’u Abubakar hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda kona masallacin, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 23.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gezawa

এছাড়াও পড়ুন:

Kotun ƙoli ta tabbatar da Okpebholo a matsayin gwamnan Edo

Kotun Ƙoli ta tabbatar da Sanata Monday Okpebholo na jam’iyyar APC a matsayin sahihin Gwamnan Jihar Edo.

Wannan hukunci ya kawo ƙarshen shari’ar da ake yi biyo bayan zaɓen gwamnan jihar da aka yi a ranar 21 ga watan Satumba, 2024.

Jami’ar Tarayya ta Gashuwa za ta ba matar Tinubu digirin girmamawa Tinubu ne ya buɗe wa Buhari ƙofar zama shugaban ƙasa — Hadimi

Kwamitin alƙalai biyar ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Mohammed Garba ne, suka yanke hukuncin a ranar Alhamis.

Sun yi watsi da ƙarar da ɗan takarar PDP, Asue Ighodalo, ya shigar, kan cewar hujjojin da ya gabatar ba su da inganci.

Mai Shari’a Garba, ya ce Ighodalo da jam’iyyarsa PDP ba su kawo hujjoji masu ƙarfi da za su nuna cewa Okpebholo bai lashe zaɓen bisa ƙa’ida ba.

Ya kuma ƙara da cewa PDP ba ta bayyana yadda hukuncin kotun ƙasa da kotun ɗaukaka ƙara suka saɓa doka ba.

Tun da farko, PDP ta ce an samu matsaloli da kura-kurai a lokacin zaɓen, kuma ta nemi kotu ta soke sakamakon.

Amma kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓe da kotun ɗaukaka ƙara sun yi watsi da ƙarar.

Hakan ne ya sa suka garzaya Kotun Ƙoli don neman haƙƙinsu.

Wannan hukunci na yau Alhamis, ya kawo ƙarshen duk wata shari’a da ta shafi zaɓen Gwamnan Jihar Edo, kuma Okpebholo zai ci gaba da zama gwamnan jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lauyoyin Natasha Sun Buƙaci Ta Koma Majalisa Ranar Talata Bayan Miƙa Takardun Hukuncin Kotu
  • Iran:  Goyon Bayan Shugaban Gwamnatin Jamus Ga ‘Yan Sahayoniya, Yin Tarayya Ne A Fada Da Iran
  • Jihohi 10 Sun Kinkimo Bashin Naira Biliyan 417 Duk Da Karin Samun Kudaden Shiga
  • Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista
  • Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
  • Kotun ƙoli ta tabbatar da Okpebholo a matsayin gwamnan Edo
  • Babban Kwamandan Sojin Iran Ya Bayyana Cewa Iran Ta Koyawa Gwamnatin Isra’ila Hankali
  • ’Yan ƙabilar Ibo ne suka fi aikata laifi a Jihar Anambra ba Fulani ba — Gwamna Soludo
  • Kazem Sajjadpour Ya ce: Iraniyawa Suna Daukan Tarayyar Turai Ma Goyon Bayan Harin Zaluncin Isra’ila Kansu
  • Tsohon Ɗan Takarar Gwamna A CPC, Haruna Sa’eed Kajuru, Ya Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Binciki Kisan ‘Yan Zariya  A Filato