Gwamnatin Kano za ta sabunta masallacin da aka kona masallata 23 a kan N150m
Published: 27th, May 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kashe Naira miliyan dari da hamsin da ɗaya da dubu dari takwas da sittin da uku (N151,863,895.97) domin sake gina wani masallaci da wani matashi ya cinna wa wuta a yayin da jama’a ke tsaka da sallar Asuba a cikin jam’i a Tiga Gadan da ke Karamar Hukumar Gezawa, a watan Mayun bara.
Aikin sabunta masallacin ya kunshi gina makarantar Islamiyya tare da ofis da bandaki da kuma rijiyar burtsatse mai amfani da hasken rana tare da tankin ruwa na sama.
Kwamishinan Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kano, Ibrahim Abdullahi Wayya, ya sanar amincewar sake gina masallacin ya biyo bayan alkawarin da Gwamna Abba Kabir ya yi a lokacin da ya ziyarci wurin da abin ya faru.
Ya yi kira ga mutanen kauyen Gadan da su saka wannan karimci ta hanyar bayar da goyon bayan da ake bukata don tabbatar da nasarar kammala aikin, da kuma samar da kariya ga sabbin gine-ginen.
Yadda kotu ta yanke wa wanda ya kona mutane a cikin masallaci hukuncin rataya a Kano Amarya ta kashe uwargida da wuka a Katsina An yanke wa wanda ya yi wa agolarsa fyaɗe ɗaurin rai-da-raiA ranar Litinin ne Babbar Kotun Musukunci ta yanke wa Shafi’u Abubakar hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda kona masallacin, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 23.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gezawa
এছাড়াও পড়ুন:
Yahudawan Sahyoniyya Sun Shiga Masallacin Al-Aksa Tare Da Rakiyar Sojoji
Duk tare da yakin da suke fafatawa a Gaza, dimbin yahudawan sahyoniyya masu bauta sun kutsa cikin masallacin Al-aksa da ke birnin Qudus inda suka gudanar da bukukuwan addinu a jiya Litinin.
Shafin yanar Gizo na labarai ‘Arab News’ ya bayyana cewa, bakin na addini, farin ciki ne da kwace gabacin birnin Qudus daga hannun falasdinawa a yakin shekara 1967 tsakanin yahudawan da kuma larabawa. Birnin Qudus ta gabas dai nan ne masallacin Al-aksa yake, kuma nan ne Falasdinawa suke da dama.
Yahudawan dai su na ganin dukkan birnin Qudus wanda ya hada har da inda masallacin Al-aksa yake mallakinsu ne kuma su na da shirin rusa masallacin don gina wurin bautansu a inda masallacin yake.