Iran Ta Yi Watsi Da Jita-Jitar Cewa Za Ta Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium
Published: 29th, May 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Dr. Isma’ila Baka’i, ya sanar a marecen jiya Laraba cewa, Iran za ta iya dakatar da tace sanadarin Uranium a karkashin yarjejniyar da za a iya kullawa da Amurka.
Kakakin ma’ikatar harkokin wajen na Jamhuriyar Musulunci ta Iran Dr. Baka’i ya yi watsi da labarin da kamfanin dillancin labarun “Reuters” ya watsa na yiyuwar dakatar da tace sanadarin “Uranium’ yana mai kara da cewa; zai ci gaba babu kakkautawa, kuma ba abinda za ma za a yi tayi ba.
Kamfanin dillancin labarun ” Mehr” na Iran ya ambato Baka’i yana cewa; labarin na Reuters, ba komai ba ne sai farfaganda ake maimaitawa, da kuma an sha kore gaskiyarta.
Kamfanin dillancin labarun na “Reuters’ kamar yadda ya saba, ya ambato wata majiya Iran, wacce bai ambata kowacece ba, tana cewa za a dakatar da tace sanadarin Uranium din na wucin gadi, saboda a sakar mata kudadenta da ake rike da su.
A lukuta da dama dai jami’an kasar Iran sun sha ambata cewa batun tace sanadarin “Urani’um” wani abu ne da za a ci gaba da yinsa a cikin Iran,an cimma yarjejeniya, ko a’a.
Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci ya bayyana cewa; Iran ba ta dauki batun tace Urani’um abin wasa ba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: da tace sanadarin
এছাড়াও পড়ুন:
An kama mutum 41 da ake zargi da kisan DPO a Kano
Rundunar ’yan sandan Jihar Kano ta ce, ta kama mutane 41 da ake zargi da hannu a kisan DPO ɗin Rano, CSP Baba Ali.
Rundunar ta bayyana lamarin, wanda ya janyo kace-nace, a matsayin harin kai tsaye kan sadaukarwar da jami’an tsaro ke yi, waɗanda suke sadaukar rayuwarsu domin kare al’umma.
NAHCON ta kammala jigilar maniyyata aikin hajjin 2025 NDLEA ta kama maniyyata aikin hajji ɗauke da hodar iblisA wata sanarwa da kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar a ranar Alhamis, ya ce rundunar ’yan sanda na aiki tuƙuru domin ganin an gurfanar da duk waɗanda ke da hannu wajen kisan, da kuma masu alaƙa da ƙone-ƙone.
Sanarwar ta ƙara da cewa, “Rundunar ta bayyana kaɗuwarta da alhini dangane da kisan gillar da aka yi wa CSP Baba Ali a lokacin da yake bakin aiki, wannan kashe-kashen na rashin hankali babban hari ne ga al’ummarmu.”
Kiyawa ya ce Kwamishinan ’yan sanda, CP Ibrahim Adamu Bakori ya tabbatar wa mazauna Jihar Kano cewa, rundunar ta ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a, kuma babu wani abin da za a bari wajen ganin an hukunta waɗanda suke da alaƙa da kisan jami’in.
Sanarwar ta ƙara da cewa, “Kwamishinan ya sake nanata cewa ’yan sanda ba za su ƙasa a gwiwa ba har sai an hukunta duk wanda ke da alaƙa da wannan ɗanyen aiki.”