Aminiya:
2025-07-24@03:27:57 GMT

Mutane 20 sun rasu a hatsari motar ’yan wasan Jihar Kano

Published: 31st, May 2025 GMT

Aƙalla mutum 20 ne aka tabbatar sun mutu sakamakon wani mummunan hatsarin mota da ya rutsa da tawagar Jihar Kano da ke dawowa daga gasar wasannin motsa jiki ta ƙasa (NSF) da aka kammala a Jihar Ogun.

Lamarin na ban tausayi ya faru ne a ranar Asabar a garin Dakatsalle, kimanin kilomita 50 daga Kano, yayin da tawagar ke gab da isa gida.

Rahotannin farko daga masu bada agajin gaggawa da shaidun gani da ido sun nuna cewa waɗanda suka rasa rayukansu a hatsarin sun haɗa da ’yan wasa da ɗan jarida, ma’aikatan lafiya da jami’an gudanar da harkokin wasanni.

Shugaban ƙungiyar marubutan wasanni ta Najeriya (SWAN) reshen Kano, Zahraddeen Saleh, ya tabbatar da wannan mummunan lamari.

Ya kuma ƙara da cewa daga cikin waɗanda suka mutu akwai Jami’in Hulɗa da Jama’a na Hukumar Wasanni ta Kano da wani mai ɗaukar hoto da ke aiki da Express Radio da wata kafar yada labarai ta intanet.

Kwamishinan Wasanni na Jihar Kano, Mustapha Rabi’u Kwankwaso, ya bayyana alhini game da lamarin, yana mai addu’ar rahama ga mamatan

Yayin da ba a kai ga gano ainihin musabbabin haɗarin ba har zuwa lokacin rubuta wannan rahoto, mahukunta sun tabbatar da cewa an hanzarta tura ƙungiyoyin bada agajin gaggawa zuwa wurin.

An kai waɗanda suka ji raunuka zuwa asibitoci mafi kusa don neman kulawar gaggawa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan wasa Hatsari

এছাড়াও পড়ুন:

Rayuwata Na Cikin Hatsari, A Dawo Min Da Jami’an Tsarona – Natasha 

“Saboda barazanar tsaro da ke tattare da al’amuran siyasa, da kuma buƙatar kare lafiyata yayin gudanar da aiki, ina roƙon a dawo min da jami’an tsarona,” in ji ta.

Ta kuma haɗa da kwafin hukuncin kotun, inda ta jaddada marnin dawo da ita bakin aiki.

Sai dai komawarta majalisa ya haifar da ce-ce-ku-ce, domin Majalisar Dattawa ta ce hukuncin kotun da Sanata Natasha ke dogaro da shi ba dole ba ne a aiwatar da shi, domin ba umarni ba ne kai-tsaye.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matasa 3 sun rasu yayin wanka a rafi a Bauchi
  • UNICEF Ya Bukaci Jihar Kano Ta Bai Wa Yara Muhimmanci A Kasafin Kudi
  • Har Yanzu Yaƙi Da Ta’addanci Ne Babban Muradin Gwamnatina — Tinubu
  • Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu
  • Zazzaɓin Lassa ya kashe mutum 151 a Nijeriya bana — NCDC
  • Rayuwata Na Cikin Hatsari, A Dawo Min Da Jami’an Tsarona – Natasha 
  • PSC Ta Amince Da Ɗaga Darajar Jami’an ‘Yan Sanda 12 Daga Matakin CP Zuwa AIG, Da Sauransu
  • Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba
  • Libya Ta Tasa Keyar Baƙin Haure Yan Kasar Sudan 700 Zuwa Kasarsu
  • Mataimakiyar Shugaban Majalisar Dinkin Duniya Ta Jinjinawa Gwamnan Kano Bisa Ayyukan Cigaban Jihar