Aminiya:
2025-11-03@04:04:43 GMT

‘’Yan bindigar birni sun karɓe shugabancin Najeriya — El-Rufai

Published: 31st, May 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya soki tsarin shugabanci na Najeriya na yanzu, inda ya bayyana cewa ‘’yan bindigar birni’ sun karɓe ragamar mulkin ƙasar.

Ya yi wannan jawabi ne a ranar Asabar a Abuja, yayin taron lacca na cika shekaru 60 da haihuwar tsohon Gwamnan Jihar Rivers, Rotimi Amaechi, mai taken ‘Amfani da Talauci a Matsayin Makami a Najeriya.

El-Rufai ya bayyana cewa a yanzu ne Najeriya take fuskantar matsalolinta mafiya muni tun bayan samar da ita da matsayin ƙasa ɗaya a shekarar 1914.

“Shi ya sa muke tare muna aiki tare da shirya wani haɗin gwiwa don dawo da Najeriya kan turbar da ta dace saboda ta riga ta kauce hanya,” in ji shi.

Mutanen da suka rasu a ambaliyar ruwa a Neja sun ƙaru zuwa 151 Maƙabarta mai shekaru 500 da ta koma maɓoyar ’yan daba 

Ya danganta yanayin da ƙasar ke ciki a yanzu da gazawar shugabanci, inda ya ce, ƙasar “ta kai ga wannan mataki ne saboda mun bar ’yan bindiga, da ke zaune a birane, ba waɗanda ke cikin daji ba, sun karɓe ragamar shugabanci.”

Tsohon gwamnan ya ci gaba da nuna damuwarsa game da abin da ya bayyana a matsayin matsalar rashin ƙwarewa a mulki.

Ya ce, “Ina ganin matsalar da muke da ita, wadda ina ganin Gwamna Babangida ya ambata, ita ce muna samun mutane marasa ƙwarewa mu miƙa musu shugabanci. Yawancinsu ba su san abin da za su yi ba. Abin da sani kawai shi ne yadda za su karɓi mulki amma ba su san yadda za su yi amfani da shi ba,” in ji El-Rufai.

Ya kammala jawabinsa da kira ga ’yan Najeriya da su tashi tsaye su zaɓi shugabannin da ke da cikakkiyar ƙwarewa da ƙarfin hali, da kuma jajircewa don ci gaban ƙasar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan bindigar birni Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Duk da cewa gwamnati na da dubban kwararrun malamai a makarantunta, har yanzu ana ganin ɗaliban makarantun gwamnati na kasa da na makarantun masu zaman kansu wajen ƙoƙari da kuma sakamakon jarabawa.

 

Wannan matsala ta daɗe tana jawo muhawara tsakanin iyaye, malamai da hukumomin ilimi.

Wasu na ganin matsaloli ne da ba za su rasa nasaba da rashin kulawa da watsi da harkar ilimi da gwamnati ta yi ba.

Ko wadanne dalilai ne suka daliban makarantun masu zaman kansu suka fi kokari idan aka kwatanta da daliban makarantu na gwamnati?

NAJERIYA A YAU: Shin Ko Sauya Hafsoshin Tsaro Zai Kawo Karshen Aikin Ta’dda A Najeriya? DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa PDP Ta Ki Sayarwa Sule Lamido Fom Din Takarar Shugaban Jam’iyya

Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci Daga Yanzu
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari