Aminiya:
2025-09-17@23:28:06 GMT

‘’Yan bindigar birni sun karɓe shugabancin Najeriya — El-Rufai

Published: 31st, May 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya soki tsarin shugabanci na Najeriya na yanzu, inda ya bayyana cewa ‘’yan bindigar birni’ sun karɓe ragamar mulkin ƙasar.

Ya yi wannan jawabi ne a ranar Asabar a Abuja, yayin taron lacca na cika shekaru 60 da haihuwar tsohon Gwamnan Jihar Rivers, Rotimi Amaechi, mai taken ‘Amfani da Talauci a Matsayin Makami a Najeriya.

El-Rufai ya bayyana cewa a yanzu ne Najeriya take fuskantar matsalolinta mafiya muni tun bayan samar da ita da matsayin ƙasa ɗaya a shekarar 1914.

“Shi ya sa muke tare muna aiki tare da shirya wani haɗin gwiwa don dawo da Najeriya kan turbar da ta dace saboda ta riga ta kauce hanya,” in ji shi.

Mutanen da suka rasu a ambaliyar ruwa a Neja sun ƙaru zuwa 151 Maƙabarta mai shekaru 500 da ta koma maɓoyar ’yan daba 

Ya danganta yanayin da ƙasar ke ciki a yanzu da gazawar shugabanci, inda ya ce, ƙasar “ta kai ga wannan mataki ne saboda mun bar ’yan bindiga, da ke zaune a birane, ba waɗanda ke cikin daji ba, sun karɓe ragamar shugabanci.”

Tsohon gwamnan ya ci gaba da nuna damuwarsa game da abin da ya bayyana a matsayin matsalar rashin ƙwarewa a mulki.

Ya ce, “Ina ganin matsalar da muke da ita, wadda ina ganin Gwamna Babangida ya ambata, ita ce muna samun mutane marasa ƙwarewa mu miƙa musu shugabanci. Yawancinsu ba su san abin da za su yi ba. Abin da sani kawai shi ne yadda za su karɓi mulki amma ba su san yadda za su yi amfani da shi ba,” in ji El-Rufai.

Ya kammala jawabinsa da kira ga ’yan Najeriya da su tashi tsaye su zaɓi shugabannin da ke da cikakkiyar ƙwarewa da ƙarfin hali, da kuma jajircewa don ci gaban ƙasar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan bindigar birni Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa