Amarya ta kashe uwargida da wuka a Katsina
Published: 27th, May 2025 GMT
’Yan sanda sun tsare wata matar aure kan zargin ta da kashe kishiyarta a Ƙaramar Hukumar Daura da ke Jihar Katsina.
Mai magana da yawun ’yan sanda a Jihar Katsina, DSP Abubakar Aliyu, ya bayyana cewa matar ta yi wa uwargidarta kisan gilla ne bayan wata hatsaniya da aka samu a tsakaninsu, wanda ya ƙazance har ya kai ga kisa.
Amaryar, mai shekara 23 a duniya, ta yi wa uwargida wannan aika-aika ne ranar Lahadi a unguwar Sabon Gari, daura da Makaranta Firamare ta Daɗi.
DSP Abubakar Aliyu, ya ce a ranar ce bayan mijinsu ya dawo daga kasuwa ya kai ƙara Babban Ofishin ’Yan Sanda da ke Daura cewa ya iske uwar gidansa kwance a cikin jini.
An yanke wa wanda ya yi wa agolarsa fyaɗe ɗaurin rai-da-rai Jama’ar gari sun kashe DPO, sun ƙona ofishin ’yan sanda a Kano NAJERIYA A YAU: Matsalolin Da Suke Tarnaki Ga Kananan Yara A Najeriya Da Hanyoyin Magance Su“Ya bayyana cewa an sossoka wa matar tasa wuƙa, lamarin da ya sa DPO ya jagoranci jami’ansa suka je aka kai ta Babban Asibitin Tarayya na Daura, inda likita ya bayyana musu cewa rai ya riga ya yi halinsa,” in ji DSP Abubakar Aliyu.
Ya bayyana cewa a yayin bincike, an kama kishiyar amaryar, kuma ta amsa cewa ita ce ta kashe uwargidar bayan sun ba hamata iska saboda wani saɓani da suka samu.
Kwamishinan ’yan sanda na Jihar Katsina, Bello Shehu ya bayyana cewa za a gurfanar da wadda ake zargin a kotu bayan an kammala bincike.
Ya kuma buƙaci jama’a da su guji hawa dokin zuci ko ɗaukar doka a hannunsu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Amarya Kishiya uwargida ya bayyana cewa
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja
“Bayan ’yansanda sun yi gaggawar shiga yankin domin kwantar da hankulan jama’a tare da dawo da zaman lafiya, a halin yanzu akwai mutane shida da ake zargi suna tsare a kan lamarin.”
Ya kara da cewa, ‘yansandan sun hada kan shugabannin al’umma da sarakunan gargajiya wajen tattaunawa, wanda hakan ya taimaka wajen kwantar da hankula.
“Bayan faruwar lamarin, sai muka gana da shugaban al’umma a wurin, sarkin gargajiya yana tare da mu, muka tattauna kuma muka yi kokarin gano abin da ya faru, suka tabbatar mana da cewa za a wanzar da zaman lafiya,” in ji shi.
Ya ce har zuwa ranar Alhamis, Kasuwar Gosa ta koma ci gaba da gudanar da ayyukanta bisa tsauraran matakan sa ido kan ‘yan sanda.
Ajao ya kara da cewa, a kokarin da ake na magance matsalar fashi da makami, wasu laifuka biyar na fashi da makami sun kai ga kama wasu mutane 17, yayin da aka kama wasu 6 da ake zargi da hannu a fashin da aka dakile a Apo da Kubwa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp