Amarya ta kashe uwargida da wuka a Katsina
Published: 27th, May 2025 GMT
’Yan sanda sun tsare wata matar aure kan zargin ta da kashe kishiyarta a Ƙaramar Hukumar Daura da ke Jihar Katsina.
Mai magana da yawun ’yan sanda a Jihar Katsina, DSP Abubakar Aliyu, ya bayyana cewa matar ta yi wa uwargidarta kisan gilla ne bayan wata hatsaniya da aka samu a tsakaninsu, wanda ya ƙazance har ya kai ga kisa.
Amaryar, mai shekara 23 a duniya, ta yi wa uwargida wannan aika-aika ne ranar Lahadi a unguwar Sabon Gari, daura da Makaranta Firamare ta Daɗi.
DSP Abubakar Aliyu, ya ce a ranar ce bayan mijinsu ya dawo daga kasuwa ya kai ƙara Babban Ofishin ’Yan Sanda da ke Daura cewa ya iske uwar gidansa kwance a cikin jini.
An yanke wa wanda ya yi wa agolarsa fyaɗe ɗaurin rai-da-rai Jama’ar gari sun kashe DPO, sun ƙona ofishin ’yan sanda a Kano NAJERIYA A YAU: Matsalolin Da Suke Tarnaki Ga Kananan Yara A Najeriya Da Hanyoyin Magance Su“Ya bayyana cewa an sossoka wa matar tasa wuƙa, lamarin da ya sa DPO ya jagoranci jami’ansa suka je aka kai ta Babban Asibitin Tarayya na Daura, inda likita ya bayyana musu cewa rai ya riga ya yi halinsa,” in ji DSP Abubakar Aliyu.
Ya bayyana cewa a yayin bincike, an kama kishiyar amaryar, kuma ta amsa cewa ita ce ta kashe uwargidar bayan sun ba hamata iska saboda wani saɓani da suka samu.
Kwamishinan ’yan sanda na Jihar Katsina, Bello Shehu ya bayyana cewa za a gurfanar da wadda ake zargin a kotu bayan an kammala bincike.
Ya kuma buƙaci jama’a da su guji hawa dokin zuci ko ɗaukar doka a hannunsu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Amarya Kishiya uwargida ya bayyana cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Wike ya rufe ofishin FIRS da Bankin Access kan rashin biyan haraji
Hukumar Kula da Babban Birnin (FCTA) Tarayya ta rufe ofishin Hukumar Tara Haraji ta Kasa (FIRS) da kuma ginin Bankin Access kan rashin biyan haraji na sama da shekaru 25.
Daraktan Kula da Filaye na Hukumar FCTA, Chijioke Nwankwoeze, ya bayyana cewa hukumar bin ginin da bankin Access yake bashin harajin shekara 35, ofishin FIRS da ke unguwar Wuse Zone 5 kuma bashin harajin shekara 25.
Babban Ofishin na FIRS na daga cikin fitattun gine-gine da Hukumar Tara Kuɗaɗen Haraji na Babban Birnin ta rufe a safiyar Litinin, kan zargin rashin biyan haraji.
Sauran sun shafa da ginin Bankin Access da da ofishin kamfanin mai Total Energy da fitaccen otel din Ibro Hotel a unguwar Wuse, da sauran wurare 4,700 a Abuja.
Rikici ya barke a taron Atiku da kungiyoyin Arewa NAJERIYA A YAU: Tasirin Dangantakar Bangaren Zartarwa Da Na Majalisa A Kan TalakaChijioke Nwankwoeze, ya bayyana cewa ginin bankin Access da matakin ya shafa, mallakin wani wani kamfani ne, inda bankin ta kama haya.
Kazalika hukumar ta kwace izinin mallakar wasu filaye a wasu fitattun unguwanni saboda matsalar rashin biyar harajin.
Daraktan Kula da Bunƙasa Birnin Abuja, Mukhtar Galadima, ya jagoranci aikin ne bayan hukumar ta fitar da sanarwar rashin biyan harajin da ya kamata.
Ya bayyana cewa ana bin kamfanin Total harajin Shekara 10, wanda ya cika a watan Maris na 2025.
Fili mai lamba 2456 da ke titin Cadastral Zone A02, a unguwar Maitama, mallakin Kamfanin Rana Taher Furniture saboda rashin biyan harajin kas ana shekara 34.
Galadima ya bayyana cewa aikin zai ci gaba a sauran unguwannin Abuja, yana mai gargaɗin waɗanda abin ya shafa su gaggauta yin abin da aya kamata, ko su kuka da kansu.
Hukumar FCDA ta tsaurara matakan karbar haraji, musamman kam dokokin da suka shafi gine-gine da mallakar kasa a ƙarƙashin Minista mai ci, Barista Nyesom Wike.
Ya bayyana cewa wajibi ne masu filayen da hukumar ta kwace su tashi nan take, su bi hanyar da ta dace domin warware duk wata matsala.