Mai ba da shawara ga jagoran juyin juya halin Musulunci ya mayar da martani ga barazanar shugaban kasar Amurka kan cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran

Ali Shamkhani mashawarcin Jagoran juyin juya halin Musulunci a fagen siyasa ya jaddada cewa: Iran kasa ce mai cin gashin kanta mai tsayayyen tsarin tsaro, al’umma masu tsayin daka, da jajayen layi.

Ya jaddada cewa, “tattaunawa hanya ce ta ci gaba da kuma kiyaye moriyar kasa da mutunci, ba kayan aiki na tilastawa ko mika wuya ba.”

Shamkhani ya rubuta a shafinsa na dandalin X cewa: “Burin isa ga cibiyoyin nukiliyar Iran da kuma ‘tarwatsa su’ ba komai ba ne illa mafarki da shugabannin Amurka da suka gabata sun kasance sun yi has ashen hakan.

Ya kara da cewa: Iran kasa ce mai cin gashin kanta, mai tsarin tsaro mai karfi, mutane masu juriya da jajayen layi. Ya kuma jaddada cewa tattaunawa ita ce hanyar samun ci gaba da kuma kiyaye moriyar kasa da mutunci, ba tilastawa ko mika wuya ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Brazil Ta Goyi Bayan Iran Kan Hakkinta Na Mallakar Makamashin Nukiliya

Kasar Brazil ta jaddada goyon bayanta ga ‘yancin Jamhuriyar Musulunci ta Iran na amfani da makamashin nukiliya na zaman lafiya

A yayin ganawarsa da sakataren kwamitin kolin tsaron kasar Iran, mataimaki na musamman ga shugaban kasar Brazil ya sanar da cewa kasarsa tana goyon bayan ‘yancin Jamhuriyar Musulunci ta Iran na yin amfani da makamashin nukiliya na zaman lafiya da kuma aiwatar da shirin inganta sinadarin Uranium don bunkasa harkokin ilimi cikin gida ta hanyar fasahar makamashin nukiliya.

A yayin ganawar tasu, Ali Akbar Ahmadian, sakataren majalisar kolin tsaron kasar Iran, da mataimaki na musamman ga shugaban kasar Brazil Celso Amorim, sun jaddada muhimmancin ci gaba da gudanar da hadin gwiwa da tuntubar juna tsakanin kasashen biyu masu cin gashin kansu, don tunkarar manufofin bai daya.

Har ila yau Ahmadian ya yi Allah wadai da laifukan gwamnatin yahudawan sahayoniyya a Gaza tare da jaddada wajabcin hadin kai tsakanin kasashe da al’ummomi da ke adawa da mulkin mallaka wajen tunkarar gwamnatin mamayar ‘yan sahayoniyya. Ya kuma jaddada cewa, bai kamata duniya ta yi shiru ba dangane da bala’in jin kai da ake ci gaba da fuskanta a zirin Gaza, yana mai kira da a hada kai wajen tunkarar masu aikata wannan ta’asa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Limamin Sallar Juma’ar Tehran Ya Jaddada Cewa: Babu Wanda Zai Dakatar Da Iran Tace Sinadarin  Uranium
  • Tarayyar Turai Ta Yi Barazanar Karin Matsin Lamba Akan “Isra’ila”
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Matsayin Iran Na Rashin Tunanin Kera Makamin Nukiliya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yi Tsokaci Kan Hanyar Warware Takaddamar Shirin Makamashin Nukiliyar Iran
  • Brazil Ta Goyi Bayan Iran Kan Hakkinta Na Mallakar Makamashin Nukiliya
  • Shugaban Kasar Amurka Ya Ce: Kasarsa Da Iran Suna Kyakkyawar Tattaunnawa A Tsakaninsu                                                                                                                       
  • Shugaban Amurka Ya Ce: Kasarsa Da Iran Suna Kyakkyawar Tattaunnawa A Tsakaninsu                                                                                                                       
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Gana Da Ministan Cikin Gida Da Gwamnonim Lardunan Iran
  • Araghchi: “Ba ma wasa game da batun inganta uranium, wanda hakkin al’ummar Iran ne”