Aminiya:
2025-05-30@07:43:44 GMT

Ambaliyar ruwa ta kashe sama da mutum 50 a Neja

Published: 29th, May 2025 GMT

Mutanen da ya zuwa yanzu ba a kai ga tantance adadinsu ba sun rasa rayukansu sakamakon wata ambaliyar ruwa da ta afka wa garin Mokwa na jihar Neja.

Mazauna yankin sun kuma ce babbar hanyar da ta hada arewaci da kudancin Najeriya da ta bi ta yankin ita ma ambaliyar ta yanke ta.

Kodayake dai har yanzu babu cikakkun bayanai a kan ambaliyar, amma mazauna yankin sun kiyasta cewa mutanen da suka rasa ransu za su kai 50.

NEJERIYA A YAU: Sai Yaushe ’Yan Najeriya Za Su Ci Gajiyar Manufofin Shugaba Tinubu? ’Yar Najeriya ta tsinci miliyan 8.2 a Saudiyya ta mayar wa da mai su

Gidaje da sauran kadarori na miliyoyin nairori ne dai suka salwanta, yayin da wasu mazauna yankin kuma ke cewa adadin wadanda suka rasun ma zai iya wuce 50, sakamakon har yanzu akwai mata da kananan yara da dama da ba a san inda suke ba.

Aminiya ta gano cewa ambaliya ta biyo bayan wani mamakon ruwan sama da aka tafka na tsawon sa’o’i a daren Laraba, inda ya cinye gidaje yayin da mutane suke tsaka da barci.

Wani mazaunin yankin mai suna Mohammed Usman, a ce tuni har an tsamo gawarwaki da dama a cikin ruwa, amma har yanzu akwai wadanda ba a kai ga gano su ba, musamman a wuraren da gidajen suka nitse baki daya.

Daraktan Yada Labarai na Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), Dr Ibrahim Audu Hussaini, ya tabbatar da faruwar ambaliyar ga Aminiya.

Ya ce har yanzu hukumar na kan aikin tattara bayanai da alkaluma kafin ta kai ga sanar da abin da ta gano.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliya Mokwa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati Ta Kammala Samar Da Fasfo Sama Da 200,000 Da Suka Yi Jinkiri

Kan batun gyaran gidajen yari kuwa, ministan ya nuna damuwa kan halin da gidan gyaran hali ke ciki, inda ya bayyana cewa fiye da fursunoni 4,000 na tsare ne saboda gazawarsu na biyan tara kamar Naira 50,000.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ambaliyar Neja ta ci mutum 12 ’yan gida daya
  • Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja
  •  Fiye Da Falasdinawa 60 Ne Su Ka Yi Shahada A Jiya Laraba
  • Gwamna Uba Sani Ya Kammala Titin Unguwar Su El-Rufai
  • HKI Ta Kai Sabbin Hare-Hare Kan Tashar Jiragen Sama Na Birnin San’a
  • Falasdinwan Akalla 16 Sojojin HKI Suka Kashe A Gaza Ya Zuwa Yanzu A Yau Laraba
  •  Nigeria: Mutane Da Yawa Sun  Rasa Rayukansu Sanadiyyar Harin Makiyaya A Jihar Benue
  • Gwamnati Ta Kammala Samar Da Fasfo Sama Da 200,000 Da Suka Yi Jinkiri
  • Sojojin Yahudawa sun Kashe Wani Matashi A Yankin Yamma Da Kogin  Jordan