Ambaliyar ruwa ta kashe sama da mutum 50 a Neja
Published: 29th, May 2025 GMT
Mutanen da ya zuwa yanzu ba a kai ga tantance adadinsu ba sun rasa rayukansu sakamakon wata ambaliyar ruwa da ta afka wa garin Mokwa na jihar Neja.
Mazauna yankin sun kuma ce babbar hanyar da ta hada arewaci da kudancin Najeriya da ta bi ta yankin ita ma ambaliyar ta yanke ta.
Kodayake dai har yanzu babu cikakkun bayanai a kan ambaliyar, amma mazauna yankin sun kiyasta cewa mutanen da suka rasa ransu za su kai 50.
Gidaje da sauran kadarori na miliyoyin nairori ne dai suka salwanta, yayin da wasu mazauna yankin kuma ke cewa adadin wadanda suka rasun ma zai iya wuce 50, sakamakon har yanzu akwai mata da kananan yara da dama da ba a san inda suke ba.
Aminiya ta gano cewa ambaliya ta biyo bayan wani mamakon ruwan sama da aka tafka na tsawon sa’o’i a daren Laraba, inda ya cinye gidaje yayin da mutane suke tsaka da barci.
Wani mazaunin yankin mai suna Mohammed Usman, a ce tuni har an tsamo gawarwaki da dama a cikin ruwa, amma har yanzu akwai wadanda ba a kai ga gano su ba, musamman a wuraren da gidajen suka nitse baki daya.
Daraktan Yada Labarai na Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), Dr Ibrahim Audu Hussaini, ya tabbatar da faruwar ambaliyar ga Aminiya.
Ya ce har yanzu hukumar na kan aikin tattara bayanai da alkaluma kafin ta kai ga sanar da abin da ta gano.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Jaridar Washington Post Ta Ce; Yeman Ta Gurguta Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Isra’ila
Jaridar Washington Post ta bayyana cewa: Cikakken gurgunta tashar jiragen ruwa na Eilat da ke haramtacciyar kasar Isra’ila ya bayyana tasirin ikon Yemen
Jaridar Washington Post ta Amurka ta tabbatar da cewa rufe tashar jiragen ruwa ta Umm al-Rashrash na karshe ya nuna tasiri da karfin hare-haren Yemen ke da shi.
A cikin wani babban rahoto da aka buga a ranar Litinin, jaridar ta lura cewa, bayanan da jami’an mamayar Isra’ila suka yi game da gurguncewar da tashar jiragen ruwa ta yi, sun bayyana a fili “cikakkiyar nasarar da ‘yan Yemen suka yi.”
Jaridar ta yi hasashen cewa: Kasar Yemen za ta iya aiwatar da sauye-sauyen dabarun yaki a yankin, inda ta yi nazari kan wasu ayyukan sojojin ruwan kasar Yemen da suka tilastawa jiragen yakin Amurka gudu daga yankin, tare da sanadin nutsewar jiragen ruwa da dama da suka sabawa umarninsu, lamarin da ya sa sojojin Amurka da na yammacin Turai suka kasa yin komai a kansu.
Jaridar ta lura cewa ayyukan Yemen sun sanya tasirin su tun farkon harin da suka kai ga jirgin ruwan jigilar gwamnatin mamayar Isra’ila a karshen shekara ta 2023, da ya tabbatar da cewa ayyukan sun ragu da kashi 90 cikin 100 cikin kankanin lokaci, kafin tashar ta kai ga barin aiki kwata-kwata.