Ambaliyar ruwa ta kashe sama da mutum 50 a Neja
Published: 29th, May 2025 GMT
Mutanen da ya zuwa yanzu ba a kai ga tantance adadinsu ba sun rasa rayukansu sakamakon wata ambaliyar ruwa da ta afka wa garin Mokwa na jihar Neja.
Mazauna yankin sun kuma ce babbar hanyar da ta hada arewaci da kudancin Najeriya da ta bi ta yankin ita ma ambaliyar ta yanke ta.
Kodayake dai har yanzu babu cikakkun bayanai a kan ambaliyar, amma mazauna yankin sun kiyasta cewa mutanen da suka rasa ransu za su kai 50.
Gidaje da sauran kadarori na miliyoyin nairori ne dai suka salwanta, yayin da wasu mazauna yankin kuma ke cewa adadin wadanda suka rasun ma zai iya wuce 50, sakamakon har yanzu akwai mata da kananan yara da dama da ba a san inda suke ba.
Aminiya ta gano cewa ambaliya ta biyo bayan wani mamakon ruwan sama da aka tafka na tsawon sa’o’i a daren Laraba, inda ya cinye gidaje yayin da mutane suke tsaka da barci.
Wani mazaunin yankin mai suna Mohammed Usman, a ce tuni har an tsamo gawarwaki da dama a cikin ruwa, amma har yanzu akwai wadanda ba a kai ga gano su ba, musamman a wuraren da gidajen suka nitse baki daya.
Daraktan Yada Labarai na Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), Dr Ibrahim Audu Hussaini, ya tabbatar da faruwar ambaliyar ga Aminiya.
Ya ce har yanzu hukumar na kan aikin tattara bayanai da alkaluma kafin ta kai ga sanar da abin da ta gano.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Duk da cewa gwamnati na da dubban kwararrun malamai a makarantunta, har yanzu ana ganin ɗaliban makarantun gwamnati na kasa da na makarantun masu zaman kansu wajen ƙoƙari da kuma sakamakon jarabawa.
Wannan matsala ta daɗe tana jawo muhawara tsakanin iyaye, malamai da hukumomin ilimi.
Wasu na ganin matsaloli ne da ba za su rasa nasaba da rashin kulawa da watsi da harkar ilimi da gwamnati ta yi ba.
Ko wadanne dalilai ne suka daliban makarantun masu zaman kansu suka fi kokari idan aka kwatanta da daliban makarantu na gwamnati?
NAJERIYA A YAU: Shin Ko Sauya Hafsoshin Tsaro Zai Kawo Karshen Aikin Ta’dda A Najeriya? DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa PDP Ta Ki Sayarwa Sule Lamido Fom Din Takarar Shugaban Jam’iyyaWannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.
Domin sauke shirin, latsa nan