An Kama Mutane 49 Da Ake Zargi Da Damfara A Jihar Kogi
Published: 30th, May 2025 GMT
PUNCH Metro ta tuna cewa a kwanakin baya jami’an hukumar EFCC shiyyar Ilorin sun kama wasu mutane 17 da ake zargi da damfarar yanar gizo a cikin hadaka a Kananan Hukumomin Ilorin da Ifelodun na jihar.
Oyewale ya ce an tare wadanda ake zargin ne a madatsar ruwa ta Asa da yankin Jami’ar Al-Hikmah da yankin Gaa-Odota da ke Ilorin da kuma yankin Ganmo da Amoyo na jihar.
“Kamen da aka yi a ranar Talata, 13 ga Mayu, 2025, ya biyo bayan bayanan sirri da aka samu wanda ya alakanta wadanda ake zargin da ayyukan damfara ta Intanet a jihar.
Sanarwar ta kara da cewa, “Kayan da aka kwato daga hannunsu da aka kama sun hada da manyan motocin alfarma guda uku, manyan wayoyin hannu da kwamfutocin tafi da gidanka”.
Kamen na baya-bayan nan ya biyo bayan wanda aka kama a makon da ya gabata wanda ya shafi mutane 47, wadanda aka kama a Ilorin da kuma Karamar Hukumar Ifelodun bisa ga bayanan sirri da suka bankado badakalar ayyukansu na intanet.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Shekaru 6: Don amfanin matasa mun inganta harkokin ilimi, noma — Gwamna Buni
A bikin cikarsa shekaru 6 cur yana mulkin Jihar Yobe, Gwamnan jihar Mai Mala Buni da aka gudanar a ranar Alhamis ɗin da ta gabata ya bayyana irin gagarumin ci gaban da aka samu akan harkokin ilimi da noma, inda ya ce akasarin waɗanda suka amfana a waɗannan fannoni guda biyu matasa ne.
Da yake jawabi a yayin wannan taro na bikin cikarsa shekaru 6 akan mulki da aka gudanar a babban ɗakin taro na Banquet da ke gidan gwamnatin Jihar a garin Damaturu tare da ma su ruwa da tsaki na Jihar.
An gano gawar direba a cikin mota a Bayelsa Mutanen da suka mutu a ambaliyar Neja sun ƙaru zuwa 88 —NSEMAGwamnan ya bayyana ƙudirinsa na ci gaba da inganta harkokin da suka shafi matasa da kuma sauran fannonin da tuni gwamnatinsa ta yi nisa cikinsu kamar fannonin noma, kiwon lafiya, kasuwanci, tsaro da makamantansu.
Taron wanda ofishin mai baiwa Gwamna shawara na musamman kan harkokin talabijin, Rediyo da kafafen yaɗa labarai na zamani, Dakta Ibrahim Yabani, ya shirya yadda gwamnan ya amsa tambayoyin da wasu al’ummomin Jihar haɗe da ‘yan jaridu da ƙungiyoyin farar hula daga ƙananan hukumomin Jihar 17 suka yi wanda nan take Gwamnan ke amsa musu tambayoyin da suka masa kai tsaye.
A nasa jawabin, Gwamna Buni ya jaddada cewa taimakawa matasa na da matuƙar muhimmanci wanda kamar yadda ya ambata hakan ne ya ba shi ƙarfin gwiwar ƙara inganta harkokin ilimi wanda matuƙar matasa sun samu Ilimi to kuwa batun zaman banza zai kau kasancewar da sun samu Ilimi mai amfani gwamnatin nada ƙarfin gwiwar samar musu da aikin yi ta kowace irin fuska.
Gwamnan ya ce, aƙalla gwamnatin Jihar a duk wata takan kashe zunzurutun kuɗi sama da Naira miliyan 600 wajen ciyar da ɗaliban makarantun kwana waɗanda dukkansu matasa ne kuma gwamnatinsa ta tura matasa sama da 100 zuwa ƙasar Indiya don samun horo akan karantun likita wanda a yanzu haka matasan sun kammala sun dawo Jihar har an samar musu aikin yi a asibitocin Jihar.
Kan ɓangaren noma ma haka lamarin yake domin gwamnatinsa ta samarwa matasan kayayyakin gudanar da noman zamani, wadda kuma kwalliya tuni ta biya kuɗin sabulu.
Haka nan ta ɓangare tsaro nan ma haka lamarin yake domin gwamnatin ta a kullum takan yi abin da ya dace dangane da harkokin na tsaro musamman ta wajen samarwa jami’an tsaron Jihar haɗe da na Sibilyan JTF kayan aikin da suka haɗa da motocin sintiri da sauransu don ganin an daƙile barazanar da masu tada ƙayar baya ke yi ga al’ummar Jihar.
Ta fuskar gina titunan karkara ma gwamnatinsa ba ta yi ƙasa a gwiwa ba kasancewar yana da matuƙar muhimmanci wajen harkokin inganta kasuwanci, aikin noma haɗa kan al’umma musamman a ƙananan hukumomin Potiskum da Damaturu da Nguru da Gashua da Geidam da aka gina musu hanyoyin mota don ƙara alatu a garuruwan da kuma gina hanyoyin karkara a ƙananan hukumomin Jihar.
Da yake amsa tambayoyi daga mahalarta taron, Buni ya bayyana cewa, yawan gina hanyoyin mota ba wai rage tsadar sufuri ba ne, har ma yana ƙara haɓaka tattalin arzikin yankunan gaba ɗaya ta hanyar sauƙaƙawa manoman kawo amfanin gonakinsu zuwa kasuwannin Jihar.