Leadership News Hausa:
2025-05-27@19:47:40 GMT

Ranar Yara: Yaran Nijeriya Farin Ciki Za Su Yi Ko Baƙin Ciki?

Published: 27th, May 2025 GMT

Ranar Yara: Yaran Nijeriya Farin Ciki Za Su Yi Ko Baƙin Ciki?

Ga shi abin ci ya yi tsadar da samun a ci sau uku yana da wajala, balle kuma a nemi mai gina jiki. Kwananan masu sayar da ƙwai suka koka saboda rashin ciki, masu kifi dai haka abin yake balle kuma masu nama.

Duk da hakan bai hana yara murmushi ba wataƙila saboda ba su da masaniyar irin wahalar da iyayensu ke sha wajen ganin sun samar musu da rayuwa mai inganci.

Lallai ya kamata ƴan majalisa su matsala ƙaimi a samar da wani yanayi ga yara musamman wajen kare su daga faɗawa ƙangin talla ko bautar aikatau ko kuma zama ƴan jagorar masu bara, hakan kuwa zai faruwa ne idan aka aiwatar da dokar kare ƴancin yara.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Arewa Bara Yara

এছাড়াও পড়ুন:

Falasdinawa 30 sun yi shahada a Wani harin Isra’ila kan wata makaranta

Bayanai daga Falasdinu na cewa wani hari da jiragen yakin Isra’ila suka kai cikin dare a wata makarantar Gaza dake zaman matsugunni ga masu neman mafaka ya yi sanadin shahadar Falasdinawa 30, ciki har da yara da dama, a cewar jami’an kiwon lafiya da na fararen hula.

Da sanyin safiyar yau litinin ne sojojin gwamnatin Isra’ila suka kai hari a makarantar Fahmi al-Jarjawi da ke yankin Daraj na zirin Gaza, inda daruruwan iyalai da suka rasa matsugunansu daga garin Beit Lahia da ke arewacin kasar da Isra’ila ke fama da hare-haren bama-bamai suka samu mafaka.  

Hukumar tsaron farar hula ta Gaza ta ce masu aikin ceto sun tsamo gawarwakinmutum 20 daga makarantar, ciki har da yara da dama.

A cewar majiyoyin yankin, wadanda harin ya rutsa da su sun hada da Mohammad al-Kasih, shugaban bincike na ‘yan sandan Hamas a arewacin Gaza, da kuma matarsa ​​da ‘ya’yansa.

Ma’aikatar lafiya ta Falasdinu ta kuma bayar da rahoton cewa, wani hari ta sama da Isra’ila ta kai kan wani gini da ke titin Thawra a birnin Gaza jim kadan kafin harin makarantar.

A cewar ma’aikatar lafiya ta Falasdinu, kusan Palasdinawa 54,000 ne aka kashe tun fara fara farmakin Isra’ila a ranar 7 ga watan Oktoba, yawancinsu mata da yara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Kasa Na Yara Jagorori Na Kasar Sin 
  • Gwamnati Ta Kammala Samar Da Fasfo Sama Da 200,000 Da Suka Yi Jinkiri
  • NAJERIYA A YAU: Matsalolin Da Suke Tarnaki Ga Kananan Yara A Najeriya Da Hanyoyin Magance Su
  • Falasdinawa 30 sun yi shahada a Wani harin Isra’ila kan wata makaranta
  • Babu Wasu Masu Juya Tinubu Ta Bayan Fage Ministan Yaɗa Labarai
  • Hare-Haren HKI Kan Wata Makaranta A Gaza Ya Kashe Mutane 46 Daga Ciki Harda Yara Kanana
  • Fasahar Shayi Ta Sin Ta Samar Da Kwanciyar Hankali Da Nishadi Ga ‘Yan Nijeriya
  • Ana zargin wani mutum da kashe ɗan maƙwabtansa a Sakkwato
  • Ruhin Yuan Longping Ya Ba Da Tabbaci Ga Samar Da Isashen Hatsi a Nahiyar Afirka