Daesh ta yi ikirarin kai hari kan gwamnatin Syria
Published: 31st, May 2025 GMT
Kungiyar ‘yan ta’adda ta Daesh ta dauki alhakin kai hari kan dakarun gwamnatin Hayat Tahrir al-Sham (HTC) na kasar Siriya, wanda shi ne irinsa na farko a kan tsoffin kawayenta tun bayan hambarar da gwamnatin Bashar al-Assad na Siriya.
A wata sanarwa da ta fitar kungiyar ta ce ta sanya “bama-bamai” kan motar dakarun da HTC ke jagoranta a lardin Suwayda da ke kudancin kasar.
Wannan dai shi ne harin farko da Daesh ta yi ikirarin doka kan sabuwar gwamnatin ta Siriya.
Kungiyar kare hakkin dan adam ta Syrian Observatory for Human Rights (SOHR) ta bayar da rahoton cewa, a yayin harin, wasu mambobi uku na runduna ta 70 na rundunar HTC sun jikkata, a yayin da suke sintiri yayin da wata nakiya da aka tayar daga nesa ta tashi a ranar Laraba.
An kuma kashe wani mutum da ke tare da wadannan sojoji a yankin hamadar da ke kewaye.
Shi dai shugaban Syria na yanzu Abu Mohammed al-Jolani tsohon jigo ne a kungiyar Al-Qaeda da Daesh.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnonin Najeriya Sun Bayyana Alhininsu Bisa Rasuwar ‘Yan Wasan Kano
Kungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF) ta bayyana alhininta bisa rasuwar wasu ‘yan wasa daga jihar Kano a wani hadarin mota.
A cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar kuma gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq ya fitar, ya ce hadarin ya faru ne yayin da tawagar jihar ke dawowa daga gasar wasanni ta kasa da aka kammala a jihar Ogun.
Kungiyar ta NGF ta mika ta’aziyyar ta ga iyalan ‘yan wasan, gwamnatin jihar Kano,da ma kasa baki daya.
Kungiyar ta roki Allah Madaukakin Sarki da Ya ji kan ‘yan wasan, Ya kuma ba iyalansu hakurin jure wannan babban rashi.
Ali Muhammad Rabi’u