Iran ta yi kira da a karfafa hadin gwiwar tattalin arziki da kasashen Afirka
Published: 26th, May 2025 GMT
Iran ta yi kira da a karfafa hadin gwiwar tattalin arziki da kasashen Afirka bisa tsarin yankin ciniki cikin ‘yanci na nahiyar
A yayin bikin karo na 62 na kafuwar kungiyar Tarayyar Afirka da aka gudanar a birnin Tehran, ministan harkokin wajen kasar Iran Seyyed Abbas Araghchi ya jaddada aniyar kasar Iran na karfafa hadin gwiwar tattalin arziki da kasashen Afirka, musamman ta hanyar yankin ciniki cikin ‘yanci na nahiyar Afirka (AfCFTA).
A cikin jawabin da ya yi ga jakadun kasashen Afirka a Iran, Araghchi ya yaba da dabi’u da tarihin gwagwarmayar al’ummar Afirka, yana mai cewa Afirka, mai al’umma biliyan 1.4, na zaman kawa a huldar tattalin arziki ga Iran.
Ya kara da cewa: “Iran da kasashen Afirka za su iya hada kai da juna saboda irin karfin da suke da shi: dimbin albarkatun kasa a bangaren Afirka da fasahohin zamani a bangaren Iran.”
Ministan harkokin wajen na Iran ya kuma tunatar da zurfafa alaka ta tarihi da ke tsakanin Iran da nahiyar Afirka, inda ya yi kira da a fadada hadin gwiwa a fannoni daban-daban: masana’antu, noma, kiwon lafiya, ilimi, makamashi, yawon bude ido, da ababen more rayuwa.
Ya yi maraba da nasarar taron koli na hadin gwiwar tattalin arziki na Iran da Afirka karo na uku da aka gudanar kwanan nan a birnin Tehran, yana mai kallon hakan a matsayin wata alama mai kyau ga makomar dangantakar bangarorin biyu.
A karshe Araghchi ya tabbatar da cewa Iran za ta tsaya kafada da kafada da nahiyar Afirka a kokarinta na samun ci gaba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: a hadin gwiwar tattalin arziki
এছাড়াও পড়ুন:
Afrika ta Kudu ta karyata ikirarin Trump na kisan kiyashin fararen fata
Afrika ta kudu ta karyata ikirarin da shugaba Donald Trump na Amurka ya yi kan cewa kasar ta aikata kisan kiyashi kan manoma fafaren fata a Afrika ta Kudun.
Ministan ‘yan sandan Afirka ta Kudu, Senzo Mchunu, ya yi fatali da ikirarin naTrump, yana mai cewa bai da tushe balle makama, in ji jaridar Daily Maverick ta Afirka ta Kudu.
Ministan ‘yan sandan Afirka ta Kudu ya fada jiya Juma’a cewa babu wani abu da ya yi kama da hakan a game da ikirarin da Trump na kisan kiyahsin fararen fata a yayin ganawarsa da shugaban Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa.
Trump dai ya nuna wani faifan bidiyo yayin ganawarsa da takwaransa na Afrika ta Kudu, inda har ma ya nuna hotunan wasu gawawaki a gefen titi, wadanda ya danganta da manoma farar fata da aka kashe.
Mista Mchunu ya ce karyar da Mista Trump ya yi na daga cikin “labarinsa na kisan kare dangi” – yana mai nuni da zarge-zargen mara tushe da shugaban Amurka ya yi na cewa akwai wani kamfen da ya bazu a Afirka ta Kudu na kashe fararen fata tare da kwace musu gonakinsu, wanda ya ce ya yi daidai da kisan kare dangi.
Awani labarin kuma wasu kafofin yada labarai sun ce wasu hotunan da Trump ya nuna basu da alaka da wani abu da ya faru kamar haka Afrika ta Kudu.
Kamfanin dinacin labaren Reuters ya ce wani hoton tsohon labarinsu ne na wani lamari da ya faru a RDC.