Iran ta yi kira da a karfafa hadin gwiwar tattalin arziki da kasashen Afirka
Published: 26th, May 2025 GMT
Iran ta yi kira da a karfafa hadin gwiwar tattalin arziki da kasashen Afirka bisa tsarin yankin ciniki cikin ‘yanci na nahiyar
A yayin bikin karo na 62 na kafuwar kungiyar Tarayyar Afirka da aka gudanar a birnin Tehran, ministan harkokin wajen kasar Iran Seyyed Abbas Araghchi ya jaddada aniyar kasar Iran na karfafa hadin gwiwar tattalin arziki da kasashen Afirka, musamman ta hanyar yankin ciniki cikin ‘yanci na nahiyar Afirka (AfCFTA).
A cikin jawabin da ya yi ga jakadun kasashen Afirka a Iran, Araghchi ya yaba da dabi’u da tarihin gwagwarmayar al’ummar Afirka, yana mai cewa Afirka, mai al’umma biliyan 1.4, na zaman kawa a huldar tattalin arziki ga Iran.
Ya kara da cewa: “Iran da kasashen Afirka za su iya hada kai da juna saboda irin karfin da suke da shi: dimbin albarkatun kasa a bangaren Afirka da fasahohin zamani a bangaren Iran.”
Ministan harkokin wajen na Iran ya kuma tunatar da zurfafa alaka ta tarihi da ke tsakanin Iran da nahiyar Afirka, inda ya yi kira da a fadada hadin gwiwa a fannoni daban-daban: masana’antu, noma, kiwon lafiya, ilimi, makamashi, yawon bude ido, da ababen more rayuwa.
Ya yi maraba da nasarar taron koli na hadin gwiwar tattalin arziki na Iran da Afirka karo na uku da aka gudanar kwanan nan a birnin Tehran, yana mai kallon hakan a matsayin wata alama mai kyau ga makomar dangantakar bangarorin biyu.
A karshe Araghchi ya tabbatar da cewa Iran za ta tsaya kafada da kafada da nahiyar Afirka a kokarinta na samun ci gaba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: a hadin gwiwar tattalin arziki
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai
Xi ya kuma bayyana cewa, saboda bambancin yanayin kasashen Sin da Amurka, ba makawa akwai wasu sabanin ra’ayi, amma baya ga kalubale da takara, ya kamata shugabannin biyu su rike shugabanci, da kuma samar da alkibla mai dacewa, don ba da damar bunkasa dangantakar Sin da Amurka ta ci gaba da tafiya cikin kwanciyar hankali.
A nasa bangare, Trump ya ce, yana farin ciki matuka bisa haduwa da dadadden abokinsa. Ya ce, “Za mu tattauna da mai girma shugaban kasar Sin Xi Jinping. Ina da imanin cewa, mun riga mun kai ga cimma matsaya daya, kuma za mu cimma karin matsaya a nan gaba. Xi Jinping wani sahihin shugaba ne mai kima.”
Ya kuma ce, “Ba shakka kasashen biyu za su kafa nagartacciyar hulda ta dogon lokaci, ina kuma farin cikin hakan tare da shugaba Xi.”
Shugabannin biyu sun shafe sa’a 1 da mintuna 40 suna tattaunwa.
A wannan rana kuma, shugaban kasar Xi Jinping ya isa kasar Korea ta Kudu, domin halartar taron kwarya-kwarya na shugabannin kungiyar raya tattalin arzikin kasashen Asia da Pasifik (APEC) karo na 32, bisa gayyatar da shugaban kasar Korea ta Kudu Lee Jae-myung ya yi masa.(Amina Xu)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA