Hare-Haren HKI Kan Wata Makaranta A Gaza Ya Kashe Mutane 46 Daga Ciki Harda Yara Kanana
Published: 26th, May 2025 GMT
Wasu hare-haren da HKI ta kai kan gaza sun fada kan wata makaranta wacce aka maida ita wurin kwana, inda ya zuwa yanzu mutane 46 suka yi shahada a yayinda wasu 31 suka ji rauni. Daga cikin wadanda suka rasa rayukansu har da yara kanana.
Tashar talabijan ta Presstv ta bayyana cewa zana ganin yara suna gudu a cikin wuta suna kokaron kubutar da kansu.
Labarin ya kara da cewa a cikin wadanda yahudawan suka kashe a Gaza, akwai Mohammad Al-kasih shugaban bangaren yansandan bincike na arewacin Gaza da Matarsa da yayansa.
Wata majiyar Palasdinawa ta bayyana cewa kafin hari a kan makarantar yahudawan sun kai hare kan wani gida a unguwar Thawra da birnin Gaza.
Manufar yahudawan dai shi ne mamayar dukkan gaza da kuma korar Falasdinawa daga yankin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Matsalolin Da Suke Tarnaki Ga Kananan Yara A Najeriya Da Hanyoyin Magance Su
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Najeriya tana cikin ƙasashen da suka fi yawan yara a duniya, a cewar Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF).
Sai dai a cewar Hukumar ta UNICEF, kusan rabin wadannan yara suna fuskantar kalubale, kama daga cin zarafi zuwa rashin samun kulawa da dai sauran su.
Wadannan matsaloli da yara suke fuskanta dai sun dade suna ci wa masu ruwa da tsaki tuwo a kwarya.
Yayin da ake bikin Ranar Yara, shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kan halin da ya yara suke ciki a yau.
Domin sauke shirin, latsa nan