Macron : Faransa za ta iya sanya takunkumi ga gwamnatin Isra’ila matukar ba ta kawo karshen killace Gaza ba
Published: 31st, May 2025 GMT
Shugaban na Faransa ya ce Faransa za ta iya sanya takunkumi ga gwamnatin Isra’ila matukar ba ta kawo karshen killace Gaza ba, inda kuma ya bukaci kasashen duniya da kada su jajirce wajen tunkarar matsalar karancin abinci a Gaza.
A wani taron manema labarai a Singapore a ranar Juma’a, Macron ya ce dole ne Turawa su “tsaurara matsayinsu na hadin gwiwa” kan Isra’ila, “idan babu wani mataki da ya dace da yanayin jin kai, a cikin sa’o’i da kwanaki masu zuwa” a zirin Gaza.
Macron ya ce, “Katange ayyukan jin kai yana haifar da yanayi mara kyau,” yayin taron manema labarai na hadin gwiwa tare da Firaministan Singapore Lawrence Wong.
Ya yi wadannan kalamai ne a daidai lokacin da gwamnatin Isra’ila ta kakaba wa Gaza takunkumin hana agajin jin kai na tsawon watanni kusan uku.
Isra’ila dai ta zargi Macron da kasancewa a cikin “yan tawaye” ga gwamnatin tel-Aviv bayan da shugaban Faransa ya ce dole ne kasashen Turai su tsaurara matakansu na hadin gwiwa kan Isra’ila idan har ba a dauki matakin jin kai ba.
Gwamnatin Isra’ila dai ta yi kunnen uwar shegu da kiraye-kirayen da kasashen duniya suka yi dangane da bala’in karancin abinci a Gaza, tana mai cewa ya ba da izinin kai kayan agajin a karkashin wani sabon tsarin hadin guiwa da Amurka.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: gwamnatin Isra ila
এছাড়াও পড়ুন:
Tarayyar Turai Ta Yi Barazanar Karin Matsin Lamba Akan “Isra’ila”
Wasu jami’an diplomasiyyar turai sun yi wa gwamnatin Benjamin Netanyahu da cewa za ta fuskanci Karin matsin lamba idan har ba ta sauya halayyarta akan Gaza ba.
Jaridar “Washington Post” ta Amurka ta ambato jami’an diplomasiyyar turai suna cewa; sabon tsarin da ake yin aiki da shi na raba kayan agaji a Gaza, ya juya ya zama harigitsi kuma ana bude wuta akan mutane da hakan ya yi sanadiyyar jikkatar Falasdinawa da dama.”
Har ila yau jami’an diplomasiyyar na turai sun ce, ko kadan ba su da aniyar bayar da kayan agajinsu ga masu tafiyar da tsarin da su ne Isra’ila da Amurka.”
Bugu da kari, majiyar diplomasiyyar ta tarayyar turai ta ci gaba da cewa; Hotunan masu ban tsoro da suke fitowa daga Gaza, sun kai musu iya wuya, ba za su iya ci gaba da jurewa ganinsu ba.”
A cikin kwanakin bayan nan dai kasashen turai sun fara yin matsin lamba akan HKI da ta bari a shigar da kayan agaji cikin yankin na Gaza da kuma yadda take ci gaba da kashe fararen hula da kuma rusau din da take yi mai yawa.
A karon farko, tun kirkirar HKI, kasar Jamus ta soki siyasar Tel Avi akan Gaza, da hakan yake nuni da yadda kasashen turai din suke kara matsin lamba.
Shugaban gwamnatin jamus Friedrich Merz ya ce; Harin da Isra’ila ta kai wa wata makaranta a Gaza, ya tashi daga karkashin fada da ta’addanci, ya zama wani abu daban.”
A can kasar ta jamus din dai jam’iyyar hamayya ta ” Green Party” ta ce; bai kamata a rika amfani da makaman kasar Jamus a yakin Gaza ba.”