‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Published: 31st, May 2025 GMT
Ya ce a nemi bayani daga wurare daban-daban kamar Kungiyar Ma’aikatan Kananan Hukumomin Nijeriya (NULGE) da Ma’aikatar Kudi, ya kara da cewa sakataren gwamnatin tarayya shi ne shugaban kwamitin aiwatar da hukuncin.
Abubuwan da mutane yawa suke gnin ya janyo jinkirta aiwatar da hukuncin shi ne, shigar da sabon sharadi daga Babban Bankin Nijeriya (CBN), wanda ke bukatar dukkanin hukumomin gwamnati 774 su bayar da akalla shekaru biyu na rahotannin kudinsu kafin su iya karbar kasafin kudadensu kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya.
Babban bankin ya bayyana cewa dole ne gwamnatocin kananan hukumomi su cika bukatun kafin su bude asusu don kura musu kudadensu kai tsaye.
Ka’idojin da aka gindaya wa kananan hukumomin ya kara janyo tsaiko wajen jinkirta aiwatar da ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi.
Ko da yake, yunkurin farko na jinkirta aiwatar da hukuncin shi ne, tsawon watanni uku da gwamnatin tarayya ta bai gwamnonin na gudanar da shirye-shirye a watan Agusta na 2024.
Gwamnatin tarayya da gwamnonin jihohi sun yarda da dakatar da aiwatar da hukuncin har da an tantance hanyoyin biyan albashi, tabbatar da ingancin aiki, da gudanar da zaben hukumomin kananan hukumomi da sauran batutuwa.
Kungiyar Shugabannin Kananan Hukumomin Nijeriya (ALGON), ta hannun sakatarenta, Muhammed Abubakar, ta yi korafin cewa rashin aiwatar da hukuncin ta ta’allaka ne bisa umarnin da ministan shari’a na tilasta wa CBN wajen bude asusu dukkan kananan hukumomi.
ALGON ta ce rashin bayar da umurnin ya kawo cikas ga fara zantar da hukuncin kotun.
A cikin wannan lamari, ana zargin wasu gwamnoni da yin amfani da ikonsu wajen musgunawa da kuma matsin lamba ga shugabannin kananan hukumomi don kar su bude asusun da za tura musu kasun kai tsaye.
Ana ce wasu gwamnan suna matukar adawa da bude asusun a CBN, kasancewar hakan zai hana su samun damar yin amfani da kudaden kananan hukumomi da suka dade suna juyawa.
Saboda haka, ana zargin sun bai wa shugabannin kananan hukumomi umurnin kar su yarda su bude asusun a Babban Banki Nijeriya.
Idan za a iya tunawa dai, ministan shari’a ya shigar da karar a kotun koli a madadin gwamnatin tarayya da kananan hukumomi 774, yana rokon kotun ta ba da cikakken ‘yanci da bayar da kudade kai tsaye ga kananan hukumomi daga asusun tarayya.
Kotun ta duba karar sannan ta amince da wannan bukata tare da bayar da umarnin cewa a dunga bai wa kananan hukumomin kasunsu kai tsaye ba tare da gwamnonin jihohi sun rike kudaden ba wanda ya saba wa tsarin dimokuradiyya.
Shari’ar mai al’kalai bakwai, wanda ke karkashin jgorancin, Mai Shari’a Emmanuel Agim, ya bayyana cewa Nijeriya na da bangarori guda uku na gwamnati, wadanda suka hada da gwamnatin tarayya, gwamnatin jiha, da gwamnatin karamar hukumu, kuma babu wata gwamnatin jiha da ke da ikon nada kwamitin riko na kananan hukumomi saboda gwamnatin karamar hukuma ana zaben ta ne karkashin tsarin dimokuradiyya.
Kotun ta ce amfani da kwamitin riko ya saba wa kundin tsarin mulki na shekarar 1999, kuma ta kara da cewa gwamnatocin jihohi suna ci gaba da jawo mummunan rudani ta hanyar kin yarda a gudanar da zaben kananan hukumomi ta hanyar dimokuradiyya a jihohisu said ai su nada kwamitin riko ko kuma su dora wadanda suka so.
Kotun koli ta umarci a gaggauta fara aiwatar da hukuncin nan take.
Bayan wata guda da yanke hukuncin, gwamnatin tarayya ta kafa kwamitin don aiwatar da hukuncin, wanda ke karkashin shugabancin sakataren gwamnatin tarayya, Sanata George Akume. Kwamitin ya kashe tsawon yana tattaunawa kuma har ya mika rahotonsa.
Duk da haka, abun mamakin shi ne, bayan wata daya da zartar da hukuncin kotun kolin wacce ta bayar da umurnin a gaggauta aiwatar da shi, amma har yanzu an kasa aiwatar da hukuncin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: aiwatar da hukuncin gwamnatin tarayya da gwamnatin a aiwatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda ambaliyar Neja ta ci mutum 12 ’yan gida daya
Wasu mutum 12 ’yan gida daya da almajirai sama da 50 na cikin mutanen da suka rasu a ambaliyar ruwan da ta afka wa yankin Tiffin Maza da Anguwan Hausawa na karamar hukumar Mokwa a jihar Neja a ranar Laraba.
Ambaliyar, wacce ta biyo bayan wani mamakon ruwan sama da aka tafka a daren na Laraba, ta kuma lalata dukiyoyi da dama, yayin da har yanzu ake ci gaba da neman wasu mutanen da suka bace.
Garin Mokwa dai ya shahara da zama wani zango na direbobin manyan motoci, wanda hakan ya sa garin ya zama daya daga cikin mafiya hada-hadar mutane a jihar ta Neja.
NAHCON ta kammala jigilar maniyyata aikin hajjin 2025 Ambaliyar ruwa ta kashe sama da mutum 50 a NejaAminiya ta gano cewa akasarin wadanda iftila’in ya fi shafa mata ne da kananan yara.
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA) ta tabbatar da mutuwar mutum 21, amma mutanen yankin sun ce wadanda suka mutu za su iya haura 60.
Daga cikin mutanen da suka rasu a ambaliyar har da wata dalibar Kwalejin Kiwon Lafiya ta Jihar Neja mai suna Binta, wacce ta je garin na Mokwa domin yin hutu, kuma tuni har an samo gawarta.
Wata ’yar yankin mai suna Hajiya Hassana Mokwa, ta shaida wa wakilinmu cewa akalla danginta 12 zuwa 13 ne suka rasu a ambaliyar, wanda kawai ya saura kuma yanzu haka yana can a kwance a asibiti ranga-ranga.
Ta kuma ce akwai wasu daliban makarantar Alkur’ani mallakin dan uwanta da su ma suka rasa ransu.
“Akwai almajirai da dama a makarantar Alkur’anin dan uwana da su ma suka rasu. Babu wanda ya saura da rai a cikin gidan, gaba daya gidan nitsewa ya yi. Idan ka je wajen yanzu, ba za ka taba tinanin ma an taba yin gini a wajen ba,” in ji Hajiya Hassana.