HausaTv:
2025-06-08@16:58:10 GMT

 Sojojin Yemen Sun Sake Kai Wa HKI Hari Da Makami Mai Linzami

Published: 27th, May 2025 GMT

Sojojin kasar Yemen sun sake kai wani hari da makali mai linzami da safiyar yau Talata wanda ya sa jiniyar gargadi ta kada a cikin yankuna da dama na HKI.

Wannan dai shi ne karo na 3 a cikin sa’o’i 24 da kungiyar Ansarullah ta Yemen ya harba wa HKI makamai masu linzami.

Sojojin HKI sun bayyana cewa, makamin da aka harbo daga Yemen ya sa jiniyar gargadi ta kada a cikin yankuna masu yawa a Falasdinu dake karkashin mamaya.

Yemen dai tana kai wa HKI hare-hare ne saboda taimaka Falasdinawa dake yi wa kisan kiyashi fiye da shekara daya da rabi,wanda kuma har yanzu bai tsaya ba.

Shugaban kungiyar Ansarullah Sayyid Abdulmalik Husi ce; matukar ba a kawo karshen yakin Yemen ba, to ba za su daina kai wa manufofin HKI hare-hare ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

“Al’ummar kasa da kasa da yawa sun sauya ra’ayinsu mai kyau game da Amurka zuwa mummunan ra’ayi, yayin da yawan masu nuna kauna ga kasar Sin ya karu.” Wani bincike da kamfanin bincike na Morning Consult na Amurka ya fitar kwanan nan ya nuna cewa, har zuwa karshen watan Mayu, yawan al’ummar duniya dake nuna kauna ga Amurka ya ragu zuwa -1.5, yayin da adadin ya karu zuwa 8.8 ga kasar Sin. Ko da yake sakamakon ya fito ne daga hukumar bincike guda daya kawai, amma yana da ma’ana sosai wajen yin kashedi, idan aka yi la’akari da cewa binciken ya shafi kasashe da yankuna fiye da arba’in, inda akasarinsu su ne muhimman abokan huldar Amurka a fannin tattalin arziki da aikin soja.

Wannan sakamakon ba wani abu ne da ya faru ba zato ba tsammani ba. Tun daga farkon bana, matakin kakaba haraji da Amurka ta dauka ba bisa ka’ida ba ya kawo jerin munanan tasirori, wanda ya haifar da illa ga tattalin arzikin duniya, kuma Amurka ita kanta ta sha wahala daga irin wannan matakin.

Su wane ne masu lalata cinikin duniya? Su wane ne masu kare ciniki cikin ’yanci? Jama’ar duniya sun sani a bayyane.

Yanzu dai kasashe da yawa sun gane cewa, manufar “Amurka gaba da kome” ba za ta haifar da kome ba sai rikice-rikice kawai, kuma mika wuya ga matakin zaluncin haraji‌ zai haifar da karin matsawa‌ kawai. Sai dai ta hanyar hadin kai, dogaro da kai da nemo cimma nasara tare ne kawai za su iya kare hakkokinsu da muradunsu da ma samun ci gaba tare. Wannan binciken jin ra’ayin jama’a gargadi ne da duniya ya yi ga Amurka, wato idan ta ci gaba da shagala da ra’ayin samun riba kan asarar wani bangare, za ta rasa dukkan kasashe masu kawance da ita. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rasha Ta Kai Wasu Munanan Hare-Hare Kan Kasar Ukraine Tare Da Janyo Mata Munanan Barna
  • Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
  •  Rasha Ta Kai Wa Ukiraniya Hari Mafi Muni Tun Farkon Yaki
  • An Kashe Sojojin HKI Da Dama Sannan Wasu Sun Ji Raune A Garin Khan Yunus A Jiya Jumma
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gargadi Kasashen Turai Kan Fuskantar Martani Daga Kasar Iran
  • Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya
  • Rasha Ta Kai Munanan Hare-hare A Kasar Ukiraniya
  • Beirut: HKI Ta Kai Hare-hare A Unguwar Dhahiya Dake Birnin Beirut
  • ‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 
  • Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma