Limamin Sallar Juma’ar Tehran Ya Jaddada Cewa: Babu Wanda Zai Dakatar Da Iran Tace Sinadarin Uranium
Published: 31st, May 2025 GMT
Limamin da ya jagoranci sallar Jumu’a a birnin Tehran ya jaddada cewa: Ba za su taba yin watsi da ‘yancin su na mallakar makamashin nukiliya na zaman lafiya ba
Limamin da ya jagoranci sallar Juma’a a birnin Tehran fadar mulkin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Ayatullah Sayyid Ahmad Khatami, ya jaddada cewa: Iran ba ta neman mallakar makamin nukiliya, kuma ba za ta yi watsi da hakkinta na amfani da makamashin nukiliya na zaman lafiya da lumana ba.
Limamin Juma’ar Ayatullah Ahmad Khatami ya bayyana cewa: Hakika dogaro da yarda da kai, a halin yanzu ta kai Iran ga duk harkokin bunkasa ci gaban kasarta, yana mai jaddada cewa: Za a ci gaba da sarrafa sinadarin Uranium a kasar Iran duk kuwa da matsayar adawa da kasashen yamma suke nunawa kan haka.
A cikin hudubar sallar Juma’ar a jiya Juma’a Ayatullah Khatami ya kara da cewa: “Al’umma sun ga yadda suke son mayar da Iran baya a fagen makamashin nukiliya, suna cewa bai kamata Iran ta kasance ta mallaki na’urar taken Uranium koda guda daya ba, amma godiya ga Allah da kokarin masana kimiyya na kasar Iran, kasar ta samu gagarumin ci gaba a wannan fanni na kimiyya.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Likitocin Iran Suna Ci Gaba Da Samun Nasara Wajen Magance Matsalar Kurmanta Da Na Bebantaka
Likitocin Iran sun yi bikin murnar nasarar da ta samu na dasa na’urar dawo da ji da inganta shi ga masu matsalar kurmantaka da raunin ji a lardin Khuzestan na kasar
Ƙaunar sana’a, dagewa, da sadaukarwa sune sirrin nasarar kowane aiki da hidimar jin kai. Waɗannan kalaman ne Farfesa Nadir Al-Saki ya fara bude jawabinsa a yayin bikin nasarar da aka yi na aikin tiyatar dashen na’urar magance matsalar Rashin ji da rauninsa sau 1,500 a lardin Khuzestan dake kudu maso yammacin ƙasar. Wadannan tiyata sun bayyana kwarewar aikin likita da basirar likitoci a lardin, wajen maido da ji da magana ga wadanda suka rasa jin tun da fari.
Bikin dai ya samu halartar likitoci da ma’aikatan jinya da yara da dama wadanda aka yi musu aikin tiyata cikin nasara, tiyatar da ta ba su damar bayyana tunaninsu da yadda suke ji a fagen rayuwa.
Hanyoyin dasa na’urar a lardin sun zama wani dandamali mai karfi ga marasa lafiya na kasashen waje, inda marasa lafiya 36 daga kasashen Iraki, Oman, Hadaddiyar Daular Larabawa, Turkey da Afghanistan suka samu waɗannan ni’imomi a fagen rayuwar bil-Adama.