Mai neman aiki ya suma bayan matarsa ta haifi ’yan uku
Published: 31st, May 2025 GMT
Wani mutum mai suna Adamu Muhammed Tenimu ya suma bayan da samu labarin cewa matarsa ta haifi jarirai ’yan uku a asibitin koyarwa na Jami’ar Tarayya da ke Lokoja babban birnin Jihar Kogi ranar Juma’a.
Shaidu sun ce, mutumin da ya ji cewa matarsa ta haifi ‘ya’ya mata uku, sai ya faɗi ya suma a harabar asibitin nan take.
Jami’an asibitin da masu jajantawa sun yi wa mutumin agaji inda cikin gaggawa aka samu ya farfaɗo.
Jim kaɗan da farfaɗowarsa, Muhammed, wanda aka ce ya kasance mai neman aikin yi na tsawon shekaru, ya ce labarin ya haɗa da farin ciki da baƙin ciki a gare shi.
Ya ce, “tunanin samun damar biyan kuɗin asibiti da kuma ɗawainiyar kuɗi na jariran da aka haifa uku ne ya dame ni. da jin labarin haihuwarsu nan take, lamarin ya sa na faɗi ƙasa na suma.”
“Na gode wa Allah da wannan abin al’ajabi, amma ina cikin ruɗani da baƙin ciki, ba mu sa ran haihuwar ’yan uku ba, a halin yanzu ba mu da kuɗi da ƙarfin biyan kuɗin asibiti, balle mu kula da jarirai uku a lokaci ɗaya.
“Wannan albarkar haihuwar tana da girma, amma hakan nauyi ne. Ba ni da ko da kuɗin sayan abincin jarirai. Ban san ta inda zan fara ba,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa, suna faman gudanar yadda za su rayu; kuma an shirya haihuwar jariri guda ɗaya ne, don haka muka gaza biyan kuɗin yin hoton cikin don sanin ‘jarirai nawa ne saboda ƙarancin kuɗi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jarirai yan uku
এছাড়াও পড়ুন:
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato
Mataimakinsa kan harkokin majalisa Honarabul Attahiru Danmadi ne ya wakilci dan majalisar ya kuma tabbatarwa wadanda lamarin ya shafa kokarinsa kan daukar matakan da suka kamata domin tabbatar da tsaron rayukan su da dawowa da zaman lafiya a yankunan.
Garuruwan da ‘yan bindigar suka tarwatsa a gundumar Kuchi sun hada da Fakku, sha’alwashi, tulluwa da Rafin- gora a inda mutane bakwai suka rasa rai. A gundumar Jabo kuwa kauyukan da lamarin ya shafa su ne; Gesolodi, Hilya, Guraye, Guma, Chakai, Modo, Badariya, Tafki, Balera, Gudumawa da Rafin shinka.
“Mun girgiza kwarai da wannan halin da kuke ciki. A matsayina na wakilin ku, zan ci-gaba da kokarin da ya kamata a majalisa domin ganin jami’an tsaro sun kawo karshen wannan ta’addancin.”
Dan Majalisar ya ce ya gabatar da bukata ga Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa domin tallafawa wadanda lamarin ya shafa kuma zai ci- gaba da bibiya domin ganin tallafin ya samu cikin lokaci.
Ya ce yana kokarin ganin rundunar sojoji ta kara tura wadatattun jami’ai tare da tallafa masu domin yakar ‘yan ta’addan da wanzar da zaman lafiya a yankunan.
Tallafin kayan abinci na gaggawa da dan majalisar ya bayar sun hada da buhuhuwan masara, gero, garin kwaki da kuma kuli- kuli.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp