Mai neman aiki ya suma bayan matarsa ta haifi ’yan uku
Published: 31st, May 2025 GMT
Wani mutum mai suna Adamu Muhammed Tenimu ya suma bayan da samu labarin cewa matarsa ta haifi jarirai ’yan uku a asibitin koyarwa na Jami’ar Tarayya da ke Lokoja babban birnin Jihar Kogi ranar Juma’a.
Shaidu sun ce, mutumin da ya ji cewa matarsa ta haifi ‘ya’ya mata uku, sai ya faɗi ya suma a harabar asibitin nan take.
Jami’an asibitin da masu jajantawa sun yi wa mutumin agaji inda cikin gaggawa aka samu ya farfaɗo.
Jim kaɗan da farfaɗowarsa, Muhammed, wanda aka ce ya kasance mai neman aikin yi na tsawon shekaru, ya ce labarin ya haɗa da farin ciki da baƙin ciki a gare shi.
Ya ce, “tunanin samun damar biyan kuɗin asibiti da kuma ɗawainiyar kuɗi na jariran da aka haifa uku ne ya dame ni. da jin labarin haihuwarsu nan take, lamarin ya sa na faɗi ƙasa na suma.”
“Na gode wa Allah da wannan abin al’ajabi, amma ina cikin ruɗani da baƙin ciki, ba mu sa ran haihuwar ’yan uku ba, a halin yanzu ba mu da kuɗi da ƙarfin biyan kuɗin asibiti, balle mu kula da jarirai uku a lokaci ɗaya.
“Wannan albarkar haihuwar tana da girma, amma hakan nauyi ne. Ba ni da ko da kuɗin sayan abincin jarirai. Ban san ta inda zan fara ba,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa, suna faman gudanar yadda za su rayu; kuma an shirya haihuwar jariri guda ɗaya ne, don haka muka gaza biyan kuɗin yin hoton cikin don sanin ‘jarirai nawa ne saboda ƙarancin kuɗi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jarirai yan uku
এছাড়াও পড়ুন:
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki
Rundunar Sojojin Nijeriya (AFN) za ta gudanar da bikin kammala aiki na tsohon Shugaban Tsaron Ƙasa (CDS), Janar Christopher Gwabin Musa (mai ritaya) a ranar Jumma’a, 31 ga Oktoba, 2025, domin girmama ayyukan da ya gudanar a lokacin hidimarsa.
A cewar sanarwar da shalƙwatar tsaro ta ƙasa (DHQ) ta fitar a ranar Alhamis, an shirya bikin Pulling Out Parade ɗin ne da ƙarfe 09:00 na safe, inda manyan hafsoshin Soja, da jami’an gwamnati da ƴan uwa za su halarta. Wannan biki na nuni da kammala aikin Soja a matakin ƙoli, kuma yana ɗaya daga cikin manyan al’adun da ake yi wa manyan jami’an da suka yi aiki da ƙwarewa da sadaukarwa.
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP Kasashen Afirka Biyar Da Suka Fi Karfin SojiJanar Musa ya yi aikin Soja na tsawon shekaru masu yawa, kuma ya yi shugabanci a matsayin Shugaban Tsaron Ƙasa daga Yuni 2023 zuwa Oktoba 2025. A wannan lokaci, ya jagoranci manyan hare-haren yaƙi da ta’addanci tare da ƙarfafa hulɗar haɗin gwuiwa tsakanin sassan Sojojin Nijeriya.
A ranar 24 ga Oktoba, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sanar da sabon tsarin jagorancin rundunar Soja, inda ya naɗa Manjo Janar Olufemi Oluyede a matsayin sabon Shugaban Tsaro, wanda hakan ya kawo ƙarshen wa’adin Janar Musa.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA