Aminiya:
2025-06-01@04:55:57 GMT

Mai neman aiki ya suma bayan matarsa ta haifi ’yan uku

Published: 31st, May 2025 GMT

Wani mutum mai suna Adamu Muhammed Tenimu ya suma bayan da samu labarin cewa matarsa ​​ta haifi jarirai ’yan uku a asibitin koyarwa na Jami’ar Tarayya da ke Lokoja babban birnin Jihar Kogi ranar Juma’a.

Shaidu sun ce, mutumin da ya ji cewa matarsa ​​ta haifi ‘ya’ya mata uku, sai ya faɗi ya suma a harabar asibitin nan take.

Zazzaɓin Lassa da sanƙarau ya kashe mutum 366 a jihohi 24 – NCDC Shekaru 6: Don amfanin matasa mun inganta ilimi da noma — Gwamna Buni 

Jami’an asibitin da masu jajantawa sun yi wa mutumin agaji inda cikin gaggawa aka samu ya farfaɗo.

Jim kaɗan da farfaɗowarsa, Muhammed, wanda aka ce ya kasance mai neman aikin yi na tsawon shekaru, ya ce labarin ya haɗa da farin ciki da baƙin ciki a gare shi.

Ya ce, “tunanin samun damar biyan kuɗin asibiti da kuma ɗawainiyar kuɗi na jariran da aka haifa uku ne ya dame ni. da jin labarin haihuwarsu nan take, lamarin ya sa na faɗi ƙasa na suma.”

“Na gode wa Allah da wannan abin al’ajabi, amma ina cikin ruɗani da baƙin ciki, ba mu sa ran haihuwar ’yan uku ba, a halin yanzu ba mu da kuɗi da ƙarfin biyan kuɗin asibiti, balle mu kula da jarirai uku a lokaci ɗaya.

“Wannan albarkar haihuwar tana da girma, amma hakan nauyi ne. Ba ni da ko da kuɗin sayan abincin jarirai. Ban san ta inda zan fara ba,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, suna faman gudanar yadda za su rayu; kuma an shirya haihuwar jariri guda ɗaya ne, don haka muka gaza biyan kuɗin yin hoton cikin don sanin ‘jarirai nawa ne saboda ƙarancin kuɗi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jarirai yan uku

এছাড়াও পড়ুন:

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

Bayan mintuna 90 na wasan ba tareda wani ya doke wani ba sai alkalin wasa ya bayar da damar bugun daga kai sai mai tsaron raga, Jamaica ta ci kwallaye 4 inda Nijeriya ta ci dukkan kwallaye 5 da yan wasan suka buga, hakan ya sa yaran na Eric Chelle suka lashe gasar Unity Cup ta bana da ta kunshi kasashen Ghana, Trinidad And Tobago, Jamaica da Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati
  • Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara
  • Indiya ta amsa cewa Pakistan ta kakkaɓo jiragen yaƙinta
  • Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano
  • An kama mutum 41 da ake zargi da kisan DPO a Kano
  • AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Gana Da Ministan Cikin Gida Da Gwamnonim Lardunan Iran
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Ayukka 16 A Sakkwato
  • NEJERIYA A YAU: Sai Yaushe ’Yan Najeriya Za Su Ci Gajiyar Manufofin Shugaba Tinubu?