Ma’aikatar kudi ta kasar Sin ta sanar a yau Litinin cewa, tun daga rubu’i na hudu na shekarar da ta gabata, gwamnatin kasar Sin ta aiwatar da matakai a jere na kula da harkokin tattalin arziki, da kyautata yanayin tattalin arzikin kasar, da kuma hasashen kwarin gwiwa da ake yi kan kasuwanni cikin kwanciyar hankali.

Matakin da kamfanin nazari na Moody’s ya dauka na tabbatar da daidaiton mizanin matsayin kasar Sin, wani lamari ne mai kyau, na kyakkyawan fatan bunkasar tattalin arzikin kasar.

 

Ma’aikatar kudin ta kasar Sin ta bayyana cewa, a mataki na gaba, wasu tsare-tsare za su gudana tare, kuma za su ci gaba da yin tasiri, da samar da cikakken goyon baya ga bunkasar tattalin arziki mai inganci. Duk yadda yanayin waje ya sauya, kasar Sin za ta kasance cike da kwarin gwiwa, kuma za ta mai da hankali kan yin abun da ya dace.(Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tare Da Taimakon Kasar China Za A Bude Masana’antun  Sarrafa Sanadarin Lithium A Nigerria

Kasar Najeriya ta sanar da Shirin fara aiki a wasu sabbin masana’antu domin sarrafa sanadarin Lithium

Ministan ma’adanai na kasar ta Najeriya Daili Alaki ne ya sanar a ranar Lahadin da ta wuce cewa, a wannan shekarar da ake ciki ta 2025, da hakan zai samar da gagarumin sauyi a fagen kayan da kasar za ta rika fitarwa zuwa kasashen waje.

Kamfanin dillancin “Reuters” ya ambato ministan ma’adanai na kasar yana ci gaba da cewa; ‘yan kasar China ne za su zuba hannun jari mafi grima a cikin wannan Shirin da hakan zai samar da ayyukan yi a cikin kasar da kuma bunkasar harkokin kere-kere.

Haka nan kuma Alaki ya yi ishara da cewa; Msana’antar sarrafa Lithium din da za a kafa akan iyakar jihohin Kaduna da Niger, za ta ci kudin da sun kai dalar Amurka miliyan 600, yayin da za a kafa wata matatar sanadarin na Lithium a  bayan birnin Abuja da kudin da sun kai dala miliyan 200.

Wata masana’antar ta sarrafa sanadarin Lithium da za kafa a tsakiyar wannan shekarar, za ta kasance ne a Jahar Nasarawa wacce ke iyaka da birnin Abuja.

  Majiyar ta kuma ambaci cewa kamfanin kasar China na ” Geoling’ da kuma “Kankakas Tecnalogy” ne su ka samar da kaso 80% na jarin  tafiyar da kamfanonin,yayin da za a samar da sauran kaso 20% daga cikin gida.

Tun a 2022 ne aka gudanar da wani bincike na karkashin kasa wanda ya tabbatar da cewa da akwai sanadarin “Lithium” a jahohi 6 na kasar, kuma yana da kyau sosai da kuma yawa,lamarin da ya ja hankalin kasashen duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Raya Al’adu Wani Sirri Ne Na Ci Gaban Kasar Sin
  • An Sake Zaben Qalibof A Matsayin Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Iran
  • Tare Da Taimakon Kasar China Za A Bude Masana’antun  Sarrafa Sanadarin Lithium A Nigerria
  • Sin Za Ta Harba Na’urar Binciken Samaniya Ta Tianwen-2
  • Iran ta yi kira da a karfafa hadin gwiwar tattalin arziki da kasashen Afirka
  • Firaministan Pakistan na ziyara Tehran mai manufar inganta dangantaka tsakanin kasashen biyu
  • Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Tsibiran Fasifik Sun Yaba Da Yadda Ake Mulkin Kasar Sin 
  • Shugaban Jam’iyyar Adawa A Burtaniya Ya Ce HKI Tana Yaki A Gaza Ne A Madadin Gwamnatin Kasar
  • Fasahar Shayi Ta Sin Ta Samar Da Kwanciyar Hankali Da Nishadi Ga ‘Yan Nijeriya