Ma’aikatar Kudi Ta Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Matsayar Kamfanin Moody’s Bisa Kiyaye Mizanin Matsayin Kasar
Published: 27th, May 2025 GMT
Ma’aikatar kudi ta kasar Sin ta sanar a yau Litinin cewa, tun daga rubu’i na hudu na shekarar da ta gabata, gwamnatin kasar Sin ta aiwatar da matakai a jere na kula da harkokin tattalin arziki, da kyautata yanayin tattalin arzikin kasar, da kuma hasashen kwarin gwiwa da ake yi kan kasuwanni cikin kwanciyar hankali.
Ma’aikatar kudin ta kasar Sin ta bayyana cewa, a mataki na gaba, wasu tsare-tsare za su gudana tare, kuma za su ci gaba da yin tasiri, da samar da cikakken goyon baya ga bunkasar tattalin arziki mai inganci. Duk yadda yanayin waje ya sauya, kasar Sin za ta kasance cike da kwarin gwiwa, kuma za ta mai da hankali kan yin abun da ya dace.(Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Dalilin da ya sa muka gayyaci Sheikh Lawal Triumph – ’Yan sanda
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta bayyana dalilin da ya sa ta gayyaci malamin addini Sheikh Lawal Triumph.
A wata sanarwa da ta fitar, ’yan sanda sun ce sun sani cewa wasu daga cikin wa’azozin da Sheikh Triumph ke yi suna haddasa rashin jituwa a tsakanin al’ummar jihar.
Ya kamata mulkin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ’yan Kudu — Hannatu Musawa Ba lallai matatun man gwamnati su sake aiki ba har abada a Najeriya – ƊangoteRundunar ta ce kowa na da ’yancin faɗin albarkacin bakinsa, amma dole ne komai ya kasance bisa doka.
Saboda haka ne Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, ya gayyaci Sheikh Lawal Triumph don tattaunawa da jami’an gwamnati, shugabannin addini da na al’umma.
Manufar ita ce a nemi hanyar hana irin wannan rikici sake faruwa a nan gaba.
Rundunar ta kuma buƙaci al’umma da su kwantar da hankalinsu su guji yin abubuwan da za su haifar da tashin hankali.
“Yana da muhimmanci a girmama ra’ayin juna da abin da mutane suka gaskata, kuma a tabbatar da cewa duk abin da mutum zai faɗa ko zai yi bai saɓa wa doka ba,” in ji rundunar.
Wannan lamari ya fara ne bayan wani wa’azi da Sheikh Lawal Triumph ya yi, wanda ya tayar da ƙura.
Ya faɗi haka ne a matsayin martani ga waɗanda suke musanta wani hadisi da ke cewa kwarkwata ƙazanta ce.
Wannan ya janyo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, inda wasu suka fara kiran a kashe Sheikh Lawal Triumph bisa zargin ya yi izgili ya Manzon Allah (S.A.W).
Rundunar ta kuma shawarci jama’a da su kai koken su ga hukumomin da suka dace, maimakon yaɗa saƙonni da za su iya tayar da hankali a shafukan sada zumunta.