Leadership News Hausa:
2025-05-30@08:38:22 GMT

AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

Published: 29th, May 2025 GMT

AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

Shugaban kwamitin kungiyar Tarayyar Afrika (AU) Mahmoud Ali Youssouf, ya nanata godiyar kungiyar bisa irin goyon bayan da kasar Sin ke ba ta da ma kasashen Afrika a muhimman bangarori kamar na cinikayya da raya ababen more rayuwa da aikin gona da kiwon lafiya da bunkasa kwarewar jami’ai.

Wata sanarwa da aka fitar jiya Laraba, ta ruwaito Mahmoud Ali Youssouf na bayyana haka ne yayin da yake bankwana da Hu Changchun, shugaban tawagar kasar Sin a AU.

Shugaban na kwamitin AU ya kuma yaba wa jajircewar Hu tare da gode wa kasar Sin dangane da gudunmuwar da ta bayar na gina Cibiyar Kandagarki da Dakile Yaduwar Cututtuka ta Afrika, da taimakonta ga aikin wanzar da zaman lafiya da sauran taimakon da take bayarwa a sauran muhimmman bangarori da suka shafi jama’a a fadin nahiyar Afrika.

Jami’an biyu sun kuma waiwayi nasarorin da aka samu karkashin taron dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afrika da ya gudana a Beijing a shekarar 2024 tare da bayyana hadin gwiwar AU da Sin a matsayin misalin cudanyar bangarori daban daban. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

Air Marshal Abubakar ya ba da misalin harin da sojin saman suka kai, inda suka dakile harin ‘yan ta’adda a sansanin soji na ‘New Marte’ da sanyin safiyar ranar 24 ga Mayu, 2025, a jihar Borno

 

A wannan rana, gungun mayakan ISWAP sun yi yunkurin kutsawa sansanin soji ta hanyar amfani da babura da jefa bama-bamai (VBIED).

 

Jiragen NAF ne ke bayar da bayanan sirri kan duk wata zirga-zirgar masu tada kayar baya a yankin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Gana Da Ministan Cikin Gida Da Gwamnonim Lardunan Iran
  • Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri
  • Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya
  • Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama
  • Shugaban  Iran na ziyarar aiki a kasar Oman
  • Shugaban Kasar Iran Ya Kai Ziyara Zuwa Kasar Oman don Karfafa Kyakkyawar Alakar Kasashen Biyu
  • Raya Al’adu Wani Sirri Ne Na Ci Gaban Kasar Sin
  • An Sake Zaben Qalibof A Matsayin Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Iran