Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Rikici ya barke a taron Atiku da kungiyoyin Arewa

Daliget sun tayar da jijiyoyin a wurin taron haɗakar siyasar tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar LP a zaben 2023, Peter Obi domin fafatawa da shuagaban kasa Bola Tinubu na Jam’iyyar APC a zaɓen 2027.

Ana tsaka da taron Kungiyar Tuntubar Siyasa ta Kasa Reshen Arewa a Abuja ne hayaniya ta kaure bayan tsohon sakataren gwamnatin Tarayya, Babachir David Lawal ya sanar da wanda suna daliget da zai wakilci Jihar Jigawa.

Rashin gamsuwar sauran daliget din jihar dadi ba suka tayar da jijiyoyin wuya, inda suka hau kan mumbari suka dauke wanada aka ayyanan suka hana shi magana da yawunsu.

Daba bisani an yi nasarar shawo kan rikicin, inda aka zabi dan tsohon gwamnan jihar, Sule Lamido, Mustapha Lamido, da wani daliget kuma suka gabatar da jawabi a madadin wakilan jihar.

Ana zargin wani mutum da kashe ɗan maƙwabtansa a Sakkwato Ko gwamnoni duka za su koma APC ba zai hana mu kayar da Tinubu a 2027 ba — Babachir An kashe matashi yayin rikici a ƙauyukan Kano

Atiku wanda ya dade yana neman takarar shugaban kasa a Najeriya yana kokarin jagorantar jam’iyyun adawa domin kayar da Tinubu a zaben na 2027, yana daga cikin fitattun ‘yan siyasar da suka shiga hadakar APC a gabanin zaben 2015.

Hadakar tasu ta kai ga dan takarar APC Muhammadu Buhari, ya yi nasarar kayar da shugaban kasa Goodluck Jonathan a lokacin. Daga bisani ya fice daga APC zuwa tsohuwar jam’iyyarsa ta PDP, inda yake hankoron cika burinsa na zama shugaban kasa.

Daga cikin wadanda ke cikin hadakar tasu Atiku har da tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi da tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya a zamanin Buhari,, Babachir David Lawal.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • CMG Ta Cimma Nasarar Gudanar Da Gasar Mutum-Mutumin Inji Ta Kasa Da Kasa
  • Jama’ar gari sun kashe DPO, sun ƙona ofishin ’yan sanda a Kano 
  • Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano
  • ‘Yansanda Sun Nemi A Kwantar Da Hankula Bayan Fashewar Wani Abu A Abuja
  • Rikici ya barke a taron Atiku da kungiyoyin Arewa
  • Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Ƴan Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Mutum 2
  • Fitaccen Fastan Kaduna Rabaran Azzaman Ya Mutu A Haɗarin Mota
  • An kashe matashi yayin rikici a ƙauyukan Kano
  • Tsadar Farashin Ƙwai Ya Sa Ƴan Nijeriya Sun Haƙura Da Cinsa