Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince Da Dokokin Ilimin Noma da Gyaran Kotunan Gargajiya
Published: 30th, May 2025 GMT
Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da dokoki guda biyu masu muhimmanci, wadanda suka hada da kafa sabuwar cibiyar karatu ta gaba da sakandare, da kuma yana gyara dokar kotunan gargajiya na jihar.
Dokar farko ta tanadi kafa Kwalejin Fasahar Noma, da ke Samaru Kataf, bisa dokar kafa Kwalejin Fasahar Noma ta shekarar 2024.
Yayin da yake gabatar da rahoton kwamitin, Barrista Mahmoud Lawal Isma’ila, dan majalisa mai wakiltar Birnin Zariya kuma Shugaban Kwamitin Ilimi na Majalisa, ya bayyana cewa wannan doka tana da nufin bunkasa koyarwa da bada horo, tare da gudanar da bincike a fannin fasahar noma.
A cewar Barrista Isma’ila, wannan kwaleji za ta kasance cibiyar kwarewa ta musamman a fannin ilimin noma, inda za a koyar da dalibai ilimin aiki da kuma na kimiyya a fannoni daban-daban na fasahar noma domin kara wadatar abinci da ci gaban yankunan karkara a jihar.
A wani ci gaban da ya shafi gargajiya, majalisar ta kuma amince da wani kudiri na gyara Dokar Kotunan gargajiya mai Lamba 9 ta shekarar 2021. Wannan gyara yana da nufin inganta yadda ake gudanar da shari’a a matakin kotunan gargajiya.
Yayin da yake gabatar da rahoton kudirin, Shugaban Kwamitin Shari’a na Majalisar, dan majalisa mai wakiltar mazabar Zonkwa, Barrista Emmanuel Bako Kantiok, ya bayyana cewa gyaran yana da nufin saukaka gudanar da shari’a tare da tabbatar da saurin yanke hukunci a cikin tsarin shari’ar gargajiya.
“Zai kawo sauyi mai kyau ga Jihar Kaduna saboda zai inganta yadda ake gudanar da shari’a”, in ji shi.
An amince da dukkan dokokin ne bayan tattaunawa da shawarwari daga kwamitoci da masu ruwa da tsaki, wanda hakan ke nuna jajircewar majalisar wajen inganta tsarin shari’a da ilimi a jihar.
SHAMSUDDEEN MANNIR ATIKU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kotunan Gargajiya
এছাড়াও পড়ুন:
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
“Bayan karbar mukaminsa na sabon kwamandan hukumar NSCDC na jihar Kano, kwamared Bala Bodinga ya umurci jami’ansa da su sadaukar da kansu ga muhimmin aiki na tabbatar da amincin muhimman kadarori da ababen more rayuwa na kasa.
“Kwamandan jihar ya ba da umarnin cewa, ba dare ba rana, cikin sa’o’i 24, dole jami’an hukumar su rika yin sintiri da sanya ido domin dakile ayyukan barayi da masu aikata laifuka a lunguna da sako na jihar,” inji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp