Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince Da Dokokin Ilimin Noma da Gyaran Kotunan Gargajiya
Published: 30th, May 2025 GMT
Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da dokoki guda biyu masu muhimmanci, wadanda suka hada da kafa sabuwar cibiyar karatu ta gaba da sakandare, da kuma yana gyara dokar kotunan gargajiya na jihar.
Dokar farko ta tanadi kafa Kwalejin Fasahar Noma, da ke Samaru Kataf, bisa dokar kafa Kwalejin Fasahar Noma ta shekarar 2024.
Yayin da yake gabatar da rahoton kwamitin, Barrista Mahmoud Lawal Isma’ila, dan majalisa mai wakiltar Birnin Zariya kuma Shugaban Kwamitin Ilimi na Majalisa, ya bayyana cewa wannan doka tana da nufin bunkasa koyarwa da bada horo, tare da gudanar da bincike a fannin fasahar noma.
A cewar Barrista Isma’ila, wannan kwaleji za ta kasance cibiyar kwarewa ta musamman a fannin ilimin noma, inda za a koyar da dalibai ilimin aiki da kuma na kimiyya a fannoni daban-daban na fasahar noma domin kara wadatar abinci da ci gaban yankunan karkara a jihar.
A wani ci gaban da ya shafi gargajiya, majalisar ta kuma amince da wani kudiri na gyara Dokar Kotunan gargajiya mai Lamba 9 ta shekarar 2021. Wannan gyara yana da nufin inganta yadda ake gudanar da shari’a a matakin kotunan gargajiya.
Yayin da yake gabatar da rahoton kudirin, Shugaban Kwamitin Shari’a na Majalisar, dan majalisa mai wakiltar mazabar Zonkwa, Barrista Emmanuel Bako Kantiok, ya bayyana cewa gyaran yana da nufin saukaka gudanar da shari’a tare da tabbatar da saurin yanke hukunci a cikin tsarin shari’ar gargajiya.
“Zai kawo sauyi mai kyau ga Jihar Kaduna saboda zai inganta yadda ake gudanar da shari’a”, in ji shi.
An amince da dukkan dokokin ne bayan tattaunawa da shawarwari daga kwamitoci da masu ruwa da tsaki, wanda hakan ke nuna jajircewar majalisar wajen inganta tsarin shari’a da ilimi a jihar.
SHAMSUDDEEN MANNIR ATIKU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kotunan Gargajiya
এছাড়াও পড়ুন:
Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
A cewar ta a cikin shekarar 2024 jihar Katsina kawai ta samu masu wannan cuta mutum 17 tare da guda biyu a karamar hukumar Danmusa a cikin wannan shekara
Haka kuma Hajiya Zulaihat Radda ya bada tabbacin cewa kowane yaro an tabbatar da ya amshi allurar Riga-kafin shan Inna
Ana jawabin wakilin asusun tallafawa yara na UNICEF na ofishin Kano, Rahama Mohammed Farah ta yabawa kokarin jihar Katsina na dawo da sabon yunkurin kawar cutar shan Inna a Nijeriya baki daya
Ya kuma bayyana cewa asusun kula da kananan yara na UNICEF Yana hadin gwiwa da gwamnatoci da hukumomi da masu ruwa da tsaki a kananan hukumomi domin ganin wajen fadakar da al’umma akan allurar Riga-kafin shan Inna a jihar Katsina.
Shima da yake jawabi shugaban hukumar lafiya a matakin farko ta Jihar Katsina Dakta Shansudeen Yahaya ya yi alkawarin cigaba da wayar da kan al’umma akan wannan cuta ta shan Inna da sauran cututtuka masu kashe yara a kananan hukumomi 34 na jihar Katsina
Wadanda suka shaida wannan bikin ranar ‘Polio’ ta duniya sun hada da hukumar lafiya ta WHO da kuma masu lalurar cutar shan Inna da wakilan asusun UNICEF da matan shugabannin kananan hukumomi 34 na jihar Katsina
ShareTweetSendShare MASU ALAKA