Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da dokoki guda biyu masu muhimmanci, wadanda suka hada da kafa sabuwar cibiyar karatu ta gaba da sakandare, da kuma yana gyara dokar kotunan gargajiya na jihar.

Dokar farko ta tanadi kafa Kwalejin Fasahar Noma, da ke Samaru Kataf, bisa dokar kafa Kwalejin Fasahar Noma ta shekarar 2024.

Yayin da yake gabatar da rahoton kwamitin, Barrista Mahmoud Lawal Isma’ila, dan majalisa mai wakiltar Birnin Zariya kuma Shugaban Kwamitin Ilimi na Majalisa, ya bayyana cewa wannan doka tana da nufin bunkasa koyarwa da bada  horo, tare da gudanar da bincike a fannin fasahar noma.

A cewar Barrista Isma’ila, wannan kwaleji za ta kasance cibiyar kwarewa ta musamman a fannin ilimin noma, inda za a koyar da dalibai ilimin aiki da kuma na kimiyya a fannoni daban-daban na fasahar noma domin kara wadatar abinci da ci gaban yankunan karkara a jihar.

A wani ci gaban da ya shafi gargajiya, majalisar ta kuma amince da wani kudiri na gyara Dokar Kotunan gargajiya mai Lamba 9 ta shekarar 2021. Wannan gyara yana da nufin inganta yadda ake gudanar da shari’a a matakin kotunan gargajiya.

Yayin da yake gabatar da rahoton kudirin, Shugaban Kwamitin Shari’a na Majalisar, dan majalisa mai wakiltar mazabar Zonkwa, Barrista Emmanuel Bako Kantiok, ya bayyana cewa gyaran yana da nufin saukaka gudanar da shari’a tare da tabbatar da saurin yanke hukunci a cikin tsarin shari’ar gargajiya.

“Zai kawo sauyi mai kyau ga Jihar Kaduna saboda zai inganta yadda ake gudanar da shari’a”, in ji shi.

An amince da dukkan dokokin ne bayan tattaunawa da shawarwari daga kwamitoci da masu ruwa da tsaki, wanda hakan ke nuna jajircewar majalisar wajen inganta tsarin shari’a da ilimi a jihar.

 

SHAMSUDDEEN MANNIR ATIKU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kotunan Gargajiya

এছাড়াও পড়ুন:

MDD Ta Gudanar Da Bikin Ranar Tunawa Da Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya Ta 2025

Shima a nasa jawabin Janar Martin Luther Agwai cewa ya yi, “Aikin wanzar da zaman lafiya na daya daga cikin muhimman aikin Majalisar Dinkin Duniya da ake iya gani, inda sama da sojoji 87,000 ke sanye da rigar wanzar da zaman lafiya da farar hula suka taka rawa a cikin wasu ayyuka 12, daga Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo zuwa Lebanon, daga Sudan zuwa Mali. Nijeriya kuma na wakiltar ayyuka guda 8.”

Wadannan jajirtattun maza da mata suna taimakawa wajen daidaita yankuna, ba wa fararen hula kariya, tallafawa tsagaita wuta, da sake gina da amana inda ta lalace.

Mahimmanci lamari shi ne, tun lokacin da aka kafa tawagar wanzar da zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya ta farko a shekara ta 1948, dakarun wanzar da zaman lafiya sun ceto mutum sama da miliyan biyu daga kasashe sama da 125 cikin ayyuka 71 da suka gudanar.

Tun da fari a jawabinsa na maraba, Jami’in Majalisar Dinkin Duniya Kuma Mai Kula Da Ayyukan Jin Kai a Nijeriya Mohammed Malick Fall, maraba da zuwan bikin cika shekaru 77 na ayyukan samar da zaman lafiya na MDD ya yi, inda ya ce “Taro ne mai muhimmanci kuma ya zo daidai da cika shekaru 80 da kafuwar Majalisar Dinkin Duniya,” in ji shi.

“A tsawon tarihinta, Majalisar Dinkin Duniya babban aikinta ga al’ummar duniya shi ne inganta zaman lafiya, tsaro, ci gaba, da mutunta bil’adama, kuma ta yi fice a wajen cimma wadannan manufofi.”

“Tun daga 1948, Majalisar Dinkin Duniya ta sa ido kan ayyukan wanzar da zaman lafiya fiye da 70, da ceton rayuka da dama da kuma yin aiki a matsayin mai magance manyan tashe-tashen hankula.

A halin yanzu, sama da dakaru 87,000 masu sanye da kaki ana tura su cikin ayyuka mabanbanta kamar 12 a duniya.

Wanzar da zaman lafiya ya kasance daya daga cikin abubuwan da Majalisar Dinkin Duniya ta fi gani da inganci.”

“Karni na 21 ya zo da qalubalen tsaro da ba a tava ganin irinsa ba kuma masu alaqa da juna. Wadannan suna bukatar sabbin hanyoyi, kakkarfan hadin gwiwa na yanki da na duniya, da kuma sake nazarin yadda muke gudanar da ayyukan zaman lafiya-musamman yayin da rarrabuwar kawuna na siyasa ke kara hana shawo kan lamarin.

Wannan shi ne dalilin da ya sa muka sanya wa taron ranar dakarun wanzar da zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya a yau, taken “Makomar wanzar da zaman lafiya,” kuma ya dace sosai, in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar
  • Shekaru 6: Don amfanin matasa mun inganta ilimi da noma — Gwamna Buni 
  • Shekaru 6: Don amfanin matasa mun inganta harkokin ilimi, noma — Gwamna Buni 
  • An Kama Mutane 49 Da Ake Zargi Da Damfara A Jihar Kogi
  • Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince Da Sabbin Kwamishinoni Biyu
  • MDD Ta Gudanar Da Bikin Ranar Tunawa Da Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya Ta 2025
  • Majalisar Nasarawa Ta Bukaci A Cire Malamai 1000 Daga Aikin Tantancewar Da Ake Yiwa Malamai
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Kasar Indiya Don Habbaka Kiwon Dabbobi
  • Adamawa Ta Amince Da Mafi Ƙarancin Albashi Na ₦70,000 Ga Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi