Leadership News Hausa:
2025-05-31@17:42:39 GMT

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (2)

Published: 30th, May 2025 GMT

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (2)

Na zauna da Manzon Allah (SAW), na zauna da Sayyidina Aliyu, na zauna da Sayyidina Hassan da Hussaini, na zauna da Sayyidina Aliyu Zainul-Abidina (Babanka), don haka tambayi duk abin da kake so.” Shi (Jabir) makaho ne a lokacin, ina cikin tambayarsa kenan (in ji Ja’afarus Sadik) sai lokacin sallah ya yi, sai ya tashi a cikin wani dan mayafi da ya daura kuma ya yafa.

Amma saboda kankancinsa duk lokacin da ya jefa shi a kafada sai ya fado alhali kuma ga babban mayafinsa a rataye a kantarsa. Sai ya yi mana sallah. Bayan gamawa na tambaye shi ya ba ni labarin Hajjin da Annabi (SAW) ya yi na karshe. Sai (Jabir) ya yi ishara da hannunsa tare da maganarsa, ya kure yatsunsa guda tara ya ce, “Annabi (SAW) ya zauna shekara tara bai yi Hajji ba, sannan ya yi izini a shekara ta 10 cewa zai yi Hajji a shekarar, sai mutane masu yawa suka taho Madina a shekarar ta 10, kowa yana so ya ga yadda Annabi (SAW) zai yi Hajji don ya yi koyi. Sai muka fita tare da shi (SAW) har muka zo Zul-hulaifa aka yi ta shirin harama.

Sai matar Sayyidina Abubakar Asma’u bintu Umaisin ta haifi dan da ya sa ma sa sunan Annabi (Muhammadu bin Abubakar). Ta aika (jaririn) zuwa wurin Annabi (SAW) kuma ta tambaye shi cewa ga shi ta haihu, yanzu ya za ta yi (da batun Hajjinta)? Annabi (SAW) ya aiko mata da amsar cewa, “Ke ma ki yi wankan harama da Hajji, daga nan ki yi kunzugu (Nafkin, wannan yana nuna macen da ba ta tsarki idan za ta yi Aikin Hajji dole sai ta yi wankan harama duk da cewa ba za ta yi sallah ko ta shiga Ka’aba ba). Sai Manzon Allah (SAW) ya yi sallah a Masallacin Zul-hulaifa, daga nan ya hau rakumarsa (Kaswa) har ta daidaita da shi a sarari. Sai na duba sarari; ga mahaya nan da masu tafiyar kasa a ko ina dama da hagunsa (SAW) iya ganina. Annabi (SAW) kuma yana tsakiyar yara (matasa), sai ya yi niyya ya daga muryarsa yana cewa “Labbaikal lahumma labbaik… zuwa karshe”, (ma’ana amsawarka ya Allah, ka ce in je Hajji kuma na amsa). Mutane su ma suka amsa. Mu dai (in ji Sayyidina Jabir), Hajji kadai (ban da Umura) muka yi niyya a lokacin, a haka muka rinka tafiya tare da Annabi (SAW) har muka zo Makka muka shiga Masallaci.

Farkon abin da Annabi ya fara yi bayan mun shigo Masallacin shi ne sumbantar Dutsen Hajarul As’wad. Sai ya fara Dawafi tare da sassarfa muma muna yi, har sai da aka yi zagaye uku sai (Annabi SAW) ya koma yin tafiya har aka yi zagaye hudu. Bayan haka, Annabi ya zo daidai Mukamu Annabi Ibrahim (AS) sai ya tsaya a bayansa, ya sa Mukamun a gabansa (tsakaninsa da Ka’aba), ya karanta ayar da ke cewa, “… Sai ku riki Mukamu Ibrahim a matsayin wurin Sallah”. Daga nan ya yi Sallar Nafila raka’a biyu, a ta farko ya karanta Kulya Ayyuhal Kafiruun, a ta biyu ya karanta Kulhuwallahu Ahad. Sai Annabi (SAW) ya koma ya sake sumbantar Hajarul As’wad. Daga nan ya fita zuwa kofar Safa, yayin da ya hau kan Safa sai ya karanta ayar da ke cewa, “Hakika Safa da Marwa alamomi ne daga alamomin Addinin Allah…” ya ce “Na fara da wanda Allah ya fara ambata”, da ya hango Ka’aba sai ya ce “La’ilaha illallahu wahdahu la shariykalahu lahul mulku wa lahul hamdu wa huwa ala kulli sha’in kadiyr. La’ilaha illallahu anjaza wa’adahu…” Sannan ya yi addu’a (idan Alhaji ya haddace wannan ya karanta, idan bai haddace ba ya karanta Subhanallahi wal-Hamdulillah wal-Lahu akbar ko ya yi ta fadin la’ilaha illallah). Bayan Annabi (SAW) ya gama addu’ar sai ya sake maimaita wannan addu’ar sau uku, sai ya sauko daga Safa ya taho Marwa.

A lokacin da ya zo kwari (tsakiyar Safa da Marwa), sai ya yi sassarfa (a nan maza ke yin sassarfa, ban da mata). Da ya hau kan Marwa sai ya tsaya ya yi addu’a kamar yadda ya yi a Safa. Haka ya rika yi har ya kammala Sa’ayin a Marwa. Sai Annabi (SAW) ya ce “Idan na sa gaba kan abu ba na dawowa, da ban zo da abin hadaya ba, sai in yi Hajjin Tamattu’i in mayar da wannan Hajjin Umura. Amma yanzu duk wanda bai zo da abin hadaya ba, ya mayar da wannan Hajjin ya zama Umura (ya kwance haramarsa, ya yi aski)”. Sahabbai suka ce “Ya Rasulallahi bai fi kwana hudu a yi Arfa ba”, Annabi (SAW) ya ce “Ku cire haramar kawai, ku yi aski.”

Ba shikenan darasin ba, za mu ci gaba a mako mai zuwa in sha Allah har da kawo darussan da hadisin yake nuna mana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mutanen da suka rasu a ambaliyar ruwa a Neja sun ƙaru zuwa 151

Adadin mutanen da suka mutu a mummunar ibtila’in ambaliya a Jihar Neja ya karu zuwa mutum 151.

Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA) ce ta sanar cewa mutane 11 sun jikkata, yayin da mutane 3,018 suka rasa matsuguninsu a ibtila’in na ƙaramar hukumar Mokwa a safiyar Asabar.

Kakakin hukumar, Ibrahim Hussaini, ya bayyana cewa ambaliyar ta shafi gidaje 265 da kuma magidanta 503.

Ya ƙara da cewa yankuna uku, da suka hada da Tiffin Maza da Anguwan Hausawa, sun nutse sakamakon ruwan sama mai ƙarfi da aka yi na tsawon sa’o’i da dare a ranar Laraba.

Maƙabarta mai shekaru 500 da ta koma maɓoyar ’yan daba Sojoji sun kashe ɗan ta’adda da aka sa ladar N100m a kansa a Borno

Wannan lamari ya faru ne watanni biyar bayan Gwamnan Jihar Neja, Umar Bago, ya sanar da cewa jihar ta samu tallafin dala miliyan 10 daga Bankin Duniya don dakile zaizayar ƙasa a wasu sassan Mokwa.

Gwamnan ya ce an tantance kwararrun ’yan kwangila don gudanar da aikin.

A ranar Juma’a, Shugaban Ƙasa Bola Tinubu a yayin miƙa ta’aziyyarsa, ya umarci Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) da hukumomin tsaro su ƙara ƙaimi wajen aikin ceto da agaji a wuraren da abin ya shafa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutanen da suka rasu a ambaliyar ruwa a Neja sun ƙaru zuwa 151
  • Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
  • Yemen: Matukar Gaza Tana Fuskantar Yaki, To Babu Tsaro A HKI
  • GORON JUMA’A 30-03-2025
  • Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa
  • Yadda ambaliyar Neja ta ci mutum 12 ’yan gida daya
  • NDLEA ta kama maniyyata aikin hajji ɗauke da hodar iblis
  • Majalisar Nasarawa Ta Bukaci A Cire Malamai 1000 Daga Aikin Tantancewar Da Ake Yiwa Malamai
  • Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi