A wani wasa da masana ke ganin zai matuƙar ƙayatarwa a gasar kofin Unity, yau Laraba za a buga wasa tsakanin manyan ƙasashen Afrika biyu Nijeriya da Ghana, ba kawai wasan ƙwallon ƙafa bane yau, kare mutunci, da ɗaukaka martabar ƙasa da kuma ramuwar gayya duk suka haɗe a wasan da za a buga a filin wasa na Gtech dake birnin Landan.

Babu kanwar lasa a cikin ƙasashen biyu in dai batu ake na taka leda a nahiyar Afrika duba da cewa dukkansu sun lashe manyan kofuna na cikin gida kuma sun nuna abinda zasu iya a fagen ƙwallon ƙafa a Duniya, Ghana ta lashe gasar AFCON ta ƙasashen Afrika sau huɗu a tarihi yayin da Nijeriya ta lashe sau uku.

Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan Trump Zai Shirya Liyafar Musamman Ga Manyan Ƴan Crypto 

Wasan na yau shi ne karo na 46 da ƙasashen biyu suka haɗu da juna, a wasannin da suka buga a baya ƙasar Ghana ce ke gaba wajen samun nasarori inda ta doke Nijeriya sau 18 aka buga canjarasa 16 sannan Nijeriya ta doke Ghana sau 12, a shekarar 2022 a wani wasa da aka buga a filin wasa na Moshood Abiola Stadium dake Abuja wanda aka tashi canjaras, hakan yayi sanadiyar kasa zuwan Nijeriya buga kofin Duniya da aka buga a ƙasar Qatar.

Wasa tsakanin Nijeriya da Ghana na ɗaya daga cikin manyan wasannin gasar, inda ake hasashen ya kasance mafi zafi da za a buga a cikin dukkan gasar kuma wanda zai sake farfaɗo da ɗaya daga cikin gasar ƙwallon ƙafa ta Afrika, Ahmed Musa, daya daga cikin ‘yan wasan da suka fi buga wa Nijeriya wasa, ya dawo cikin tawagar duk da cewar bai samu gayyata domin buga wasannin share fagen shiga gasar cin kofin Duniya da aka buga a baya-bayan nan ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

HKI Ta Kai Sabbin Hare-Hare Kan Tashar Jiragen Sama Na Birnin San’a

Majiyoyin labarai a kasar Yemen sun bayyana cewa HKI ta kai hare-hare a kan tashar Jiragen sama a birnin San’aa inda a wannan karon suka lalata hanyar tashin jiragen sama a tashar.

Tashar talabijan ta Al-manar ta kasar Lebanon ta kanalto majiyar HKI tana tabbatar da wannan labarin.

Tashar radio ta HKI ta nakalto ministan yakin HKI Yasra’il Katz yana tabbatar da wannan labarin ya kuma kara da cewa hare-haren ta sama sun wargaza wani bangare na tashar jiragen sama na birnin, sannan ya lalata jirgin sama tilo wanda ya rage a tasahr jiragen.

Hakama tasha ta 12 ta HKI ta nakalto Katz yana cewa jiragen yaki fiye da 10 ne suka yi aikin hare-hare a kan tashar jirage na Sa’aa.

Kafin haka dai sojojin kasar Yemen a jiya Talata ma sun cilla makamai masu linzami samfurin Bilistic zuwa kan  tashar jiragen sama na Bengerion don tallafawa mutanen Gaza wadanda HKI take kashewa da yunwa da kuma wuta ta ko ina.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri
  • Araghchi: “Ba ma wasa game da batun inganta uranium, wanda hakkin al’ummar Iran ne”
  • HKI Ta Kai Sabbin Hare-Hare Kan Tashar Jiragen Sama Na Birnin San’a
  • Wata Hajiya ‘Yar Nijeriya Mai Shekaru 75 Ta Rasu A Saudiyya Yayin Aikin Hajji
  • Sojojin Sudan Sun Fatattaki Dakarun Kai Daukin Gaggawa Daga Sansaninsu Da Ke Birnin Omdurman
  • CMG Ta Cimma Nasarar Gudanar Da Gasar Mutum-Mutumin Inji Ta Kasa Da Kasa
  • Yahudawan Sahyoniyya Sun Shiga Masallacin Al-Aksa Tare Da Rakiyar Sojoji
  • Ranar Yara: Yaran Nijeriya Farin Ciki Za Su Yi Ko Baƙin Ciki?
  • Ba dole sai na zama shugaban Nijeriya ba — Peter Obi