Aminiya:
2025-05-30@07:10:47 GMT

Ko kwabo ban ciyo bashi ba tun da na zama Gwamnan Kaduna – Uba Sani

Published: 29th, May 2025 GMT

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya ce tun da ya hau kujerar mulki shekaru biyu da suka wuce ko kwabo bai ciyo ba a matsayin bashi.

Ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da wasu ’yan jaridu a Kaduna ranar Alhamis, albarkacin cikarsa shekaru biyu a mulki.

A cewar Gwamnan, bankuna da dama sun tunkare shi suna neman ya ci bashi amma ya ki saboda ba ya so ya ci gaba da dilmiyar da jihar a kangin bashi.

Ambaliyar ruwa ta kashe sama da mutum 50 a Neja ’Yar Najeriya ta tsinci miliyan 8.2 a Saudiyya ta mayar wa da mai su

Gwamnan ya ce a maimakon haka, ya ma rage kudaden alawus-alawus na Sakataren Gwamnatin jihar da ma na Kwamishinoninsa domin ganin an rage facaka da kudaden gwamnati.

Ya ce, “Sakataren gwamnatina tsohon Babban Sakatare ne a gwamnatin tarayya, kuma tsohon ma’aikacin Hukumar Kula da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya (FAO). Wasu daga cikin Kwamishinonina kuna suna karbar albashi mai tsoka a wuraren aikinsu na baya.

“Hakan ne ya sa na roke su da su yi hakuri da wasu alawus-alawus din su sannan su yi amfani tsofaffin motocin da gwamnatin baya ta yi amfani da su. Haka muka yi muka ci gaba da tafiyar da gwamnatinmu ba tare da ciyo bashi ba ko daya ba,” in ji Uba Sani.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Uba Sani Ya Kammala Titin Unguwar Su El-Rufai

Gwamna Uba Sani ya amsa da cewa gwamnati ta kashe sama da Naira biliyan 100 cikin watanni shida don magance matsalar ƙarancin ruwa a faɗin jihar, tare da alƙawarin cewa za a maye gurbin dukkan kayan aikin da suka lalace. Ya ƙara da cewa an riga an kashe sama da Naira miliyan 400 wajen gyara da maye gurbin bututun ruwa da aka lalata, kuma kafin ƙarshen shekara Kaduna za ta fara samun ruwa ba tare da katsewa ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince Da Sabbin Kwamishinoni Biyu
  • Ɗalibai sun maƙale lokacin da gini ya rufta suna jarrabawa
  • Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi
  • Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana
  • Gwamna Uba Sani Ya Kammala Titin Unguwar Su El-Rufai
  • Kotu ta ci su El-Rufa’i tarar miliyan 900
  • Tinubu na neman ciyo bashin Naira tiriliyan 39 daga kasashen waje
  • Raya Al’adu Wani Sirri Ne Na Ci Gaban Kasar Sin
  • Abacha Ya Shirya Kashe Ni, Abiola da Yar’Adua A Gidan Yari – Obasanjo