Ko kwabo ban ciyo bashi ba tun da na zama Gwamnan Kaduna – Uba Sani
Published: 29th, May 2025 GMT
Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya ce tun da ya hau kujerar mulki shekaru biyu da suka wuce ko kwabo bai ciyo ba a matsayin bashi.
Ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da wasu ’yan jaridu a Kaduna ranar Alhamis, albarkacin cikarsa shekaru biyu a mulki.
A cewar Gwamnan, bankuna da dama sun tunkare shi suna neman ya ci bashi amma ya ki saboda ba ya so ya ci gaba da dilmiyar da jihar a kangin bashi.
Gwamnan ya ce a maimakon haka, ya ma rage kudaden alawus-alawus na Sakataren Gwamnatin jihar da ma na Kwamishinoninsa domin ganin an rage facaka da kudaden gwamnati.
Ya ce, “Sakataren gwamnatina tsohon Babban Sakatare ne a gwamnatin tarayya, kuma tsohon ma’aikacin Hukumar Kula da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya (FAO). Wasu daga cikin Kwamishinonina kuna suna karbar albashi mai tsoka a wuraren aikinsu na baya.
“Hakan ne ya sa na roke su da su yi hakuri da wasu alawus-alawus din su sannan su yi amfani tsofaffin motocin da gwamnatin baya ta yi amfani da su. Haka muka yi muka ci gaba da tafiyar da gwamnatinmu ba tare da ciyo bashi ba ko daya ba,” in ji Uba Sani.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar
Ministan tsaro na kasar Venezuela Vladimir Padrino López ya gargadi gwamnatin Amurka dangane da duk wani kokari na kaiwa kasar Venuzuela hare hare saboda kifar da gwamnatin shugaba Nicolas Madoro. Tare da fakewa da fasakorin kwayoyi.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Vladimir yana cewa take-taken gwamnatin Amurka na sojojin da ta kawo a teken carebian ya yi kama da takalar yaki ne da kasar Venezuela , kuma idan haka ne, to sojojin sa a shirye suke su fuskance su, su kumakare kasarsu.
Kamfanin dillancin labaran IP nakasar Iran ya bayyana cewa, Amurka ta fara kai ruwa rana da gwamnatin shugaba Madoro ne tun lokacinda shugaban Amurka Donal Trump ya bayyana shugaban kasar ta Venezuela a matsayin dan kwaya kuma mai fasa korin kwayoyi.
A halin yanzu dai gwamnatin Trump ta tura sojojinta zuwa tekun Carabian kusa da kasar ta Venezuela da nufin kifar da gwamnatin Nicolas Madoro.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila September 16, 2025 Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya September 16, 2025 Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan: Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci