Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota
Published: 31st, May 2025 GMT
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp.কীওয়ার্ড: Wasa
এছাড়াও পড়ুন:
Mutane 20 sun rasu a hatsari motar ’yan wasan Jihar Kano
Aƙalla mutum 20 ne aka tabbatar sun mutu sakamakon wani mummunan hatsarin mota da ya rutsa da tawagar Jihar Kano da ke dawowa daga gasar wasannin motsa jiki ta ƙasa (NSF) da aka kammala a Jihar Ogun.
Lamarin na ban tausayi ya faru ne a ranar Asabar a garin Dakatsalle, kimanin kilomita 50 daga Kano, yayin da tawagar ke gab da isa gida.
Rahotannin farko daga masu bada agajin gaggawa da shaidun gani da ido sun nuna cewa waɗanda suka rasa rayukansu a hatsarin sun haɗa da ’yan wasa da ɗan jarida, ma’aikatan lafiya da jami’an gudanar da harkokin wasanni.
Shugaban ƙungiyar marubutan wasanni ta Najeriya (SWAN) reshen Kano, Zahraddeen Saleh, ya tabbatar da wannan mummunan lamari.
Ya kuma ƙara da cewa daga cikin waɗanda suka mutu akwai Jami’in Hulɗa da Jama’a na Hukumar Wasanni ta Kano da wani mai ɗaukar hoto da ke aiki da Express Radio da wata kafar yada labarai ta intanet.
Kwamishinan Wasanni na Jihar Kano, Mustapha Rabi’u Kwankwaso, ya bayyana alhini game da lamarin, yana mai addu’ar rahama ga mamatan
Yayin da ba a kai ga gano ainihin musabbabin haɗarin ba har zuwa lokacin rubuta wannan rahoto, mahukunta sun tabbatar da cewa an hanzarta tura ƙungiyoyin bada agajin gaggawa zuwa wurin.
An kai waɗanda suka ji raunuka zuwa asibitoci mafi kusa don neman kulawar gaggawa.