Aminiya:
2025-06-16@16:08:40 GMT

Yadda ambaliyar Neja ta ci mutum 12 ’yan gida daya

Published: 30th, May 2025 GMT

Wasu mutum 12 ’yan gida daya da almajirai sama da 50 na cikin mutanen da suka rasu a ambaliyar ruwan da ta afka wa yankin Tiffin Maza da Anguwan Hausawa na karamar hukumar Mokwa a jihar Neja a ranar Laraba.

Ambaliyar, wacce ta biyo bayan wani mamakon ruwan sama da aka tafka a daren na Laraba, ta kuma lalata dukiyoyi da dama, yayin da har yanzu ake ci gaba da neman wasu mutanen da suka bace.

Garin Mokwa dai ya shahara da zama wani zango na direbobin manyan motoci, wanda hakan ya sa garin ya zama daya daga cikin mafiya hada-hadar mutane a jihar ta Neja.

NAHCON ta kammala jigilar maniyyata aikin hajjin 2025 Ambaliyar ruwa ta kashe sama da mutum 50 a Neja

Aminiya ta gano cewa akasarin wadanda iftila’in ya fi shafa mata ne da kananan yara.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA) ta tabbatar da mutuwar mutum 21, amma mutanen yankin sun ce wadanda suka mutu za su iya haura 60.

Daga cikin mutanen da suka rasu a ambaliyar har da wata dalibar Kwalejin Kiwon Lafiya ta Jihar Neja mai suna Binta, wacce ta je garin na Mokwa domin yin hutu, kuma tuni har an samo gawarta.

Wata ’yar yankin mai suna Hajiya Hassana Mokwa, ta shaida wa wakilinmu cewa akalla danginta 12 zuwa 13 ne suka rasu a ambaliyar, wanda kawai ya saura kuma yanzu haka yana can a kwance a asibiti ranga-ranga.

Ta kuma ce akwai wasu daliban makarantar Alkur’ani mallakin dan uwanta da su ma suka rasa ransu.

“Akwai almajirai da dama a makarantar Alkur’anin dan uwana da su ma suka rasu. Babu wanda ya saura da rai a cikin gidan, gaba daya gidan nitsewa ya yi. Idan ka je wajen yanzu, ba za ka taba tinanin ma an taba yin gini a wajen ba,” in ji Hajiya Hassana.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliya Mokwa a ambaliyar

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe

An fargabar cewa ’yan bindiga sun kashe akalla mutum 100 a wani hari da suka kai a garin Yelewata da ke yankin Karamar Hukumar Guma a Jihar Benuwe.

Aminiya ta ruwaito cewa maharan sun far ma al’ummar garin na Yelewata ne a cikin daren ranar Juma’a wayewar garin Asabar.

Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa

Wadanda suka shaida harin na Yelewata sun ce maharan sun mamayi garin ne kafin karfe 12 na dare, inda suka kwashe sama da sa’a biyu suna ta’annati ba tare da wani dauki daga jami’an tsaro ba.

Da yake zantawa da Kamfanin Dillancin Labarai na AFP, wani mai magana da yawun fadar gwamnatin Benuwe, Tersoo Kula, ya tabbatar da faruwar lamarin yana mai cewa maharan sun kone gidaje da dama.

Sai dai ya ce jami’an gwamnati da suka kai ziyara yankin na Yelwata sun samu cewa wadanda aka kashe ba su wuce mutum 45 ba.

Shi ma mai magana da yawun ’yan sandan jihar, Udeme Edet, ya ce jami’ansu sun yi musayar wuta da maharan.

Haka kuma, an wani harin na daban da ya auku an kashe sojoji biyu a garin Daudu, shi ma a yankin karamar hukumar ta Guma.

Wannan harin shi ne na uku a baya-bayan nan a garin Yelewata wanda ke kan iyakar jihar ta Benuwe da Nasarawa a cikin mako daya.

Ana iya tuna cewa a watan da ya gabata ne wasu mahara da ake zargin makiyaya ne suka kashe kimanin mutum 20 a karamar hukumar Gwer ta Yamma a jihar ta Benuwe.

Kungiyar Amnesty mai fafutikar kare hakkin dan Adam ta yi kira ga gwamnatin da ta dauki matakin dakile zubar jini da salwantar rayukan al’umma a kasar.

Amnesty ta ce gazawar gwamnatin Nijeriyar ce ta sanya asarar rayukan al’ummar kasar ta zama ruwan dare.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan Asalin Tudun Loess
  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
  • Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka