Kasar Chile Na Shirin Yanke Alakar Diplomasiyya Da “Isra’ila”
Published: 29th, May 2025 GMT
Jaridar Vadiot Ahranot ta HKI ta buga labarin dake cewa; Shugaban kasar Chile Gabriel Boric ya bayar da umarni a janye jami’an diplomasiyyarsa kasarsa masu kula da alakar soja daga ofishin jakadancin kasar tasa a Tel Aviv.
Ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Chile ta wallafa wani sako a shafinta na “Internet” cewa; Ofishin jakadancin nata ya sanar da mahukunta wannan haramtacciyar cewa sun janye jami’an diplomasiyyar biyu.
Kasar ta Chile ta bayyana dalilinta na yin haka da cewa, shi ne yanayin da mutane Gaza suke ciki ta fuskar jin kai ta tabarbarewar harkokin rayuwa saboda yakin da Isra’ila take yi. Haka nan kuma kin amincewar “Isra’ila” da a shigar da kayan agaji cikin yankin na zirin Gaza.
Ita dai kasar Chile tana cikin wadanda su ka yi ta kira ga “Isr’ila” da ta datakar da yakin da take yi a Gaza, sannan kuma ta bari a shigar da kayan agaji cikin yankin.
A bisa rahoton jaridar ta Yedioy Ahranot, kasar Chile tana da jami’an soja uku a ofishin jakadancinta da su ne na ruwa, kasa da sama, amma tun watanni biyu da su ka gabata aka janye daya daga cikinsu, yanzu kuma aka jane biyun da su ka saura.
Ana sa ran cewa a ranar Lahadi mai zuwa da shugaban kasar ta Chile za iyi jawabin shekara-shekara ga al’ummar kasar, zai sanar da yanke alakar diplomasiyya da HJKI.
A gefe daya, Falasdinawa sun yaba da matakin da kasar ta Chile ta dauka na janye jami’an diplomasiyyarta daga HKI tre da bayyana shi da cewa; mataki ne mai muhimmanci da kuma nuna jarunta domin nuna kin amincewa da laifukan da HKI take tafkawa a Falasdinu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar ta Chile kasar Chile
এছাড়াও পড়ুন:
Hukumar Kare Hakkin Bil’adam Ta MDD Ta Bukaci A Kawo Karshen Kissan Kiyashi A Gaza
Shugaban hukumar kare hakkin bil’adama na MDD ta bukaci kasashen duniya su takurawa HKI ta kawo karshen kissan kiyashin da take yi a gaza bayan hare-haren da ta kai a kan wata makaranta a unguwar Fahmi Aljarjawi a cikin birnin Gaza wanda ya kashe falasdinawa akalla 36.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Francesca Albanese tana fadar haka a shafinta na X a jiya Litinin. Ta kuma kara da cewa an kashe mutane da yawa, kuma an kashe yara da yawa. An kona su da ransu, a cikin makarantar inda suke mafaka a ciki.
Albanese ta hada da hotunan bidio wanda suke nuna irin yadda wuta take kona Falasdinawa a cikin makarantar, ta turasu a shafin nata. Ta kara da cewa dole ne mu tsaida wuta a gaza kuma falasdinawa su gafarta mana kan cewa mun kasa yin haka har abin ya kai wannan matsayin.