HausaTv:
2025-07-24@04:25:21 GMT

 Kasar Chile Na Shirin Yanke Alakar Diplomasiyya Da “Isra’ila”

Published: 29th, May 2025 GMT

Jaridar Vadiot Ahranot ta HKI  ta buga labarin dake cewa; Shugaban kasar Chile Gabriel Boric ya bayar da umarni a janye jami’an diplomasiyyarsa kasarsa masu kula da alakar soja daga ofishin jakadancin kasar tasa a Tel Aviv.

Ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Chile ta wallafa wani sako a shafinta na “Internet” cewa; Ofishin jakadancin nata ya sanar  da mahukunta wannan haramtacciyar cewa sun janye jami’an diplomasiyyar biyu.

Kasar ta Chile ta bayyana dalilinta na yin haka da cewa, shi ne yanayin da mutane Gaza suke ciki ta fuskar jin kai ta tabarbarewar harkokin rayuwa saboda yakin da Isra’ila take yi. Haka nan kuma kin amincewar “Isra’ila” da a shigar da kayan agaji cikin yankin na zirin Gaza.

Ita dai kasar Chile tana cikin wadanda su ka yi ta kira ga “Isr’ila” da ta datakar da yakin da take yi a Gaza, sannan kuma ta bari a shigar da kayan agaji cikin yankin.

A bisa rahoton jaridar ta Yedioy Ahranot, kasar Chile tana da jami’an soja uku a ofishin jakadancinta da su ne na ruwa, kasa da sama, amma tun watanni biyu da su ka gabata aka janye daya daga cikinsu, yanzu kuma aka jane biyun da su ka saura.

Ana sa ran cewa a ranar Lahadi mai zuwa da shugaban kasar ta Chile za iyi jawabin shekara-shekara ga al’ummar kasar, zai sanar da yanke alakar diplomasiyya da HJKI.

A gefe daya, Falasdinawa sun yaba da matakin da kasar ta Chile ta dauka na janye jami’an diplomasiyyarta daga HKI tre da bayyana shi da cewa; mataki ne mai muhimmanci da kuma nuna jarunta domin nuna kin amincewa da laifukan da HKI take tafkawa a Falasdinu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar ta Chile kasar Chile

এছাড়াও পড়ুন:

A Kalla Falasdinawa 10 Yunwa Ta Kashe A Gaza A Cikin Sa’o’i 24

Ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta sanar da cewa a cikin sa’o’i 24 da su ka gabata adadin falasdinawan da su ka yi shahada saboda yunwa sun kai 10.

 Daga lokacin da HKI ta fara amfani da yunwa a matsayin makamin yaki,adadin falasdinawan da su ka yi shahada sun kai 111.

Wannan adadin yana nuni da yadda rashin abinci ya tsananta a cikin yankin na Gaza saboda yadda Isra’ila ta killace yankin ta hana a shigar da abinci a ciki.

A gefe daya, HKI tana ci gaba da kashe Falasdinawa ta hanyar yi musu kisan kiyashi, da a yau kadai fiye da mutane 80 ne su ka yi shahada. Mafi yawancin wadanda su ka yi shahada a cikin sa’oin nan na baya suna a unguwannin Tallul-Hawa, da Deir-Balah. Haka nan kuma ‘yan sahayoniyar sun kai wasu hare-haren a sansanin ‘yan hijira dake Mukhayyam-Shadhi.

 Kungiyoyin kasa da kasa suna ta ci gaba da yin kira da a bude iyakokin Gaza domin a shigar da kayan abinci, sai dai babu faruwar hakan.

A cikin zirin Gaza dai, mutane suna faduwa suna  somewa, wani lokaci mutuwa saboda yunwa, ba kuma babba babu yaro.

Mafi yawancin mutanen da suke mutuwa dai kananan yara ne, jarirai da matasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • A Kalla Falasdinawa 10 Yunwa Ta Kashe A Gaza A Cikin Sa’o’i 24
  • Pezeshkian: Tunanin Kawo Karshen Shirin Nukiliyar Iran Ya Yi Kama Da Tabuwa
  • Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu
  • Fizishkiyan: Batun Kare Hakkin Bil’adama Ba Komai Ba Ne Sai Karya
  •  Iran Ta Yi Kira Ga “FIFA” Da Ta Kori “Isra’ila” Daga Cikinta
  • Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh
  • Shirin Ba Da Horo A Kasar Sin Ya Taimaka Wa Inganta Masana’antar Gyadar Senegal
  • Ana Iya Samun Masu Samar Da Kayayyaki Iri-Iri Cikin Awa Daya A Kasar Sin
  • Tsoffin Jami’an ‘Yan Sanda Sun Bukaci A fitar Da Su Daga Cikin Shirin Fansho
  • MDD Ta Gargaɗi Isra’ila Kan Tilasta Wa Al’ummar Deir al-Balah Na Gaza Tashi