HausaTv:
2025-07-23@22:38:01 GMT

Yuhudawan Sahayoniyya ‘Yan Kaka Gida Sun Kutsa Cikin Masallacin Al-Aqsah

Published: 29th, May 2025 GMT

Yahudawan sahayoniyya suna ci gaba da yin kutse cikin Masallacin Al-Aqsa, yayin da kungiyar Hamas ta yi kira da a kalubalance su

Daruruwan yahudawan sahayoniyya ‘yan kaka gida a safiyar yau Alhamis suka kutsa cikin harabar Masallacin Al-Aqsa, karkashin kariyar da ‘yan sandan gwamnatin mamayar Isra’ila, yayin da ake ci gaba da kiraye-kirayen gudanar da taron gangami da kuma jaddada rashin amincewa da keta hurumin alkiblar musulmi na farko, kuma daya daga cikin Masallatai masu daraja na al’ummar musulmin duniya.

 Majiyoyin daga Qudus sun ba da rahoton cewa: Tsagerun yahudawan sahayoniyya mazauna matsugunai da dama sun gudanar da rangadi masu tayar da hankali a harabar Masallacin Al-Aqsa mai albarka, ciki har da gudanar da ibadar Talmud da raye-rayen neman tsokana.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Matasa 3 sun rasu yayin wanka a rafi a Bauchi

Wasu matasa uku daga ƙauyen Durum sun rasu yayin da suke wanka a wani rafi a ƙauyen Jinkiri, cikin gundumar Tirwun a Ƙaramar Hukumar Bauchi.

Matasan su ne; Habibu Mohammed mai shekaru 16, Abubakar Mohammed mai shekaru 16, da kuma Zailani Sule mai shekaru 14.

2027: Obi zai iya takara ba tare da ni ba — Datti Baba-Ahmed NEDC ta raba wa mutanen da ambaliya ta shafa kayan gini a Yobe

kakakin rundunar ’yan sandan Jihar, CSP Mohammed Ahmed Wakil, ya bayyana wa manema labarai faruwar lamarin.

Duk da ƙoƙarin da aka yi na ceto su, matasan sun rasu kafin a kai su asibiti.

Wakil, ya ce bincike ya nuna cewa matasan sun yi aikin haƙar ma’adinai, wanda daga bisani suka yanke shawarar yin wanka a rafin.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyayen mamatan.

Ya kuma ja hankalin jama’a kan muhimmancin guje wa wanka a irin waɗannan wurare masu hatsari.

CSP Wakil ya ce an miƙa wa iyayen matasan gawarwakinsu domin yi musu jana’iza, bayan da likitoci sun tabbatar da rasuwarsu.

Rundunar ta ce za ta ci gaba da wayar da kan jama’a da ɗaukar matakan kare rayuka, domin hana irin wannan mummunan lamari sake faruwa a nan gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Fegin Mahe Sun Yi Zanga-zanga Kan Kisan Jama’a Da ‘Yan Bindiga Ke Yi
  • A Kalla Falasdinawa 10 Yunwa Ta Kashe A Gaza A Cikin Sa’o’i 24
  • Matasa 3 sun rasu yayin wanka a rafi a Bauchi
  • Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Na Isra’ila Da Makami Mai Linzami Nau’in Flasdinu
  • Yahudawan Sahayoniyya Sun Bullo Da Dabarar Kisa Kan Falasdinawa Musamman ‘Yan Gudun Hijira
  • Jami’an Kasashen Rasha, China, Iran Sun Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa A Tehran
  • Tsoffin Jami’an ‘Yan Sanda Sun Bukaci A fitar Da Su Daga Cikin Shirin Fansho
  • Magudnar Ruwa Ta Yi Ajalin Rayuka Hudu A Zangon Kaya, Kano
  • Birgediya Janar Sabahi Fard Ya Jaddada Cewa: Duk Wani Sabon Hari Kan Iran Zai Fuskanci Martani Mai Gauni