Leadership News Hausa:
2025-06-19@02:07:07 GMT

An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC

Published: 28th, May 2025 GMT

An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC

A jiya Talata ne aka fitar da sanarwar hadin gwiwa ta taron kolin ASEAN-Sin-GCC karo na farko a birnin Kuala Lumpur fadar mulkin kasar Malaysia. Sanarwar ta ce bangarorin uku sun amince hulda, da mu’amalar al’adu, da kuma hadin gwiwar tattalin arziki tsakanin kungiyar tarayyar kasashen kudu maso gabashin Asiya wato ASEAN, da Sin, da kuma kwamitin hadin gwiwar kasashen Larabawa na yankin Gulf wato GCC na da dogon tarihi, don aka ana fatan kara inganta dangantakar sassan uku karkashin jagorancin ka’idoji, da ra’ayoyi, da manufofi, da alkawuran da aka cimma matsaya daya kan su, ciki har da tsarin dokokin MDD.

 

A cikin sanarwar, an kuma yabawa kasar Sin, bisa muhimmiyar gudummawa da take bayarwa wajen inganta zaman lafiya, da kwanciyar hankali, da wadata, da kuma ci gaba mai dorewa a yankuna da duniya baki daya, da ma yadda ta damu da yanayin da ake ciki a yankin Gabas ta Tsakiya, tare da yin Allah wadai da dukkan hare-hare da ake kaiwa fararen hula. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan kashe-kashen Benuwe — Atiku

Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar, ya yi Allah-wadai da kashe-kashen mutanen da ake yi a Jihar Benuwe, yana mai bayyana lamarin a matsayin mummunar masifa.

Cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, Atiku ya caccakin gwamnatin Nijeriya da cewa ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan lamarin.

Tinubu ya bayar da umarnin binciken hare-haren Benuwe Iran ta rataye mutumin da ta kama yana yi wa Isra’ila leƙen asiri

Ya nuna damuwa matuƙa kan ci gaba da zubar da jini a jihar Benue, yana mai kira ga gwamnatin tarayya da ta ɗauki matakin gaggawa domin kawo karshen matsalar tsaro da ke addabar yankin.

Atiku ya ce al’ummar Benuwe na fama da hare-hare na tsawon shekaru, inda rayuka ke salwanta, kauyuka ke lalacewa, iyalai ke rasa muhallansu.

“Abin da muke buƙata shi ne samun zaman lafiya da noma ba tare da fargabar mutuwa ba, da kuma bai wa ’ya’yansu tarbiyya cikin kwanciyar hankali,” in ji Atiku.

Ya jaddada cewa wadannan hakkoki ne da Kundin Tsarin Mulki na Kasa ya tanada, kuma wajibi ne gwamnati ta kare su.

Ya kuma yi Allah-wadai da yadda jami’an tsaro ke amfani da karfi da hayaki mai sa hawaye wajen tarwatsa masu zanga-zangar lumana a Benue da ke neman kariya daga gwamnati.

“Wannan ba salon mulki ba ne, illa zalunci ne da cin amanar shugabanci kuma ya nuna yadda gwamnati ta yi biris da kukan jama’a.”

Atiku ya ƙara da cewa matsalar tsaro ba a Benuwe kaɗai take ba, har da jihohin Filato da Zamfara da Kaduna da kuma Taraba, inda jama’a ke fuskantar irin wannan hali.

Ya bukaci shuwagabanni da gwamnatocin jihohi da su mayar da hankali kan kare rayukan ‘yan ƙasa fiye da yin fito na fito da siyasa, ta hanyar aiki da hukumomin tsaro da samar da kayan aiki masu inganci ga yankunan da abin ya shafa.

Hakazalika, Atiku ya yi kira ga ’yan Nijeriya da kada su yi shiru a kan zalunci. Ya bukace su da su ɗaga murya su nemi adalci da ɗaukar mataki.

Tuni dai Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bai wa mahukunta umarnin bincike da gano waɗanda ke da alhakin kai munanan hare-haren da suka janyo salwantar rayukan fiye da mutum 100 a Jihar Benuwe.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nijeriya za ta fara fitar ta tataccen mai zuwa Asia — Matatar Dangote
  • “Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki
  • Hare-haren Benuwe: Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a asibiti 
  • Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran
  • Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
  • Yaƙin Iran da Isra’ila: Amurka za ta tura jami’anta don tattaunawa da Tehran
  • Matatar man Isra’ila ta daina aiki bayan sabon harin Iran
  • Gwamnati ta kasa ɗaukar matakin da ya dace a kan kashe-kashen Benuwe — Atiku
  • An Daddale Tarin Yarjejeniyoyi Yayin Taron Baje Kolin Harkokin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka