Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Ayukka 16 A Sakkwato
Published: 29th, May 2025 GMT
A wani babban ci gaba na kawo sauyi a tsarin kiwon lafiyar Najeriya, gwamnatin tarayya ta yi ta kaddamar da ayyuka 16 a asibitin masu tabin hankali na gwamnatin tarayya dake Kware a jihar Sokoto.
Da yake jawabi a wajen bikin kaddamarwar, Ministan Kasa a ma’aikatar Lafiya da walwalar jama’a, Dokta Iziak Salako, ya jaddada cewa ayyukan na daga cikin ajandar sabuwar fata ta gwamnati shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu na karfafa cibiyoyin kiwon lafiya na kasa.
Ya ce FG ta himmatu wajen samar wa asibitoci kayayyakin more rayuwa, kayan aiki da kudade, da tallafi don inganta ayyukan hidima a fadin kasar.
Dakta Salako ya ci gaba da bayyana cewa, gwamnatin tarayya ta samar da muhimman ayyuka sama da 500 na samar da ababen more rayuwa tare da samar da ingantattun kayan aikin jinya ga manyan cibiyoyin kiwon lafiya a fadin kasar nan.
Ministan ya kuma bayyana cewa FG ta dauki ma’aikatan lafiya sama da 15,000 aiki a karkashin shirin bunkasa sana’o’in da ake yi.
Dokta Salako ya ce ma’aikatar lafiya ta fara aiwatar da dokar kula da lafiyar kwakwalwa ta Najeriya, 2023, da nufin samar da cikakken sashen kula da lafiyar kwakwalwa a wani yunkuri na hada ayyukan kula da lafiyar kwakwalwa cikin harkokin kiwon lafiya na farko a fadin kasar nan.
Rediyon Najeriya da ke Sokoto ya rawaito cewa sabbin ayyukan da aka kaddamar sun hada da dakin gwaje-gwaje na Molecular, Sashen Kula da Lafiyar Jama’a, ICU, Cibiyar Kula da Dogaro da Magungunan Mata da Yara na Yanki, Cibiyar Ba da Agajin Gaggawa, Dakunan kwanan dalibai da yawa, Makarantar Koyon kula da masu tabin hankali, ICT da dai sauransu.
Shima da yake nasa jawabin, kwamishinan lafiya na jihar Sokoto, Dakta Faruku Wurno, ya nanata kudurin jihar na yin hadin gwiwa da asibitin ta Kware, inda ya bayyana yadda tsarin kula da lafiya na asibitin zai karfafa hadin gwiwa da bayar da hidima.
Dokta Wurno ya yabawa Daraktan kula da lafiya na asibitin Farfesa Shehu Sale bisa jajircewarsa da ya yi, ya kuma bukaci wadanda suka gaje shi da su kara azama kan taswirar ci gaban da aka riga aka shimfida.
NASIR MALALI
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kware Sakkwato kula da lafiyar kula da lafiya kiwon lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Mai Martaba Sarkin Kazaure Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’o’i Na Musamman Ga Kasarsu
An bukaci Maniyyatan Jihar Jigawa su yi addu’o’i ga jihar da kasa Najeriya domin samun zaman lafiya a yayin zaman su a kasa Mai tsarki.
Amirul Hajj na Jihar, Mai Martaba Sarkin Kazaure Dr Najib Hussaini Adamu yayi wannan kiran a lokacin da yake jawabi ga Maniyyatan Jihar a Kasar Saudi Arabia.
Amirul hajjin ya hori Maniyyatan da suyi addu’a tare da karkatar da zukatansu ga dabi’u nagari, inda ya bayyana cewar canza dabi’u tare da komawa ga Allah ne kadai hanyar da za’a bi don magance matsalolin da suka addabi kasa Najeriya.
Dr Najib Hussaini Adamu, yace Allah ya albarkaci Jihar Jigawa da ni’imomi da dama, a don haka ya bukace su da su kara karfafa addu’o’i.
Kazalika, Sarkin ya kuma yabawa tallafin da gwamnati jihar ta bayar domin tabbatuwar aiwatar da hajjin bana.
A don haka, yayi kira ga Maniyyatan da su yi wa gwamnatin Jihar jigawan addu’a.
Ya kuma bukace su da su zama masu bin dokokin kasar saudiyya, yana mai horan su da su zamo masu tsafta kuma jakadu nagari a ko ina musamman a zaman Muna.
Mai Martaba ya kuma kara jan hankulansu da su zama abin misali a wajen kula da tsaftar muhalli yana mai fatan Allah yasa ayi ibada lafiya a koma gida lafiya.
Usman Mohammad Zaria