Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-09-17@21:51:31 GMT

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Ayukka 16 A Sakkwato

Published: 29th, May 2025 GMT

A wani babban ci gaba na kawo sauyi a tsarin kiwon lafiyar Najeriya, gwamnatin tarayya ta yi  ta kaddamar da ayyuka 16 a asibitin masu tabin hankali na gwamnatin tarayya dake Kware a jihar Sokoto.

 

Da yake jawabi a wajen bikin kaddamarwar, Ministan Kasa a ma’aikatar Lafiya da walwalar jama’a, Dokta Iziak Salako, ya jaddada cewa ayyukan na daga cikin ajandar sabuwar fata ta gwamnati shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu na karfafa cibiyoyin kiwon lafiya na kasa.

 

Ya ce FG ta himmatu wajen samar wa asibitoci kayayyakin more rayuwa, kayan aiki da kudade, da tallafi don inganta ayyukan hidima a fadin kasar.

 

Dakta Salako ya ci gaba da bayyana cewa, gwamnatin tarayya ta samar da muhimman ayyuka sama da 500 na samar da ababen more rayuwa tare da samar da ingantattun kayan aikin jinya ga manyan cibiyoyin kiwon lafiya a fadin kasar nan.

 

Ministan ya kuma bayyana cewa FG ta dauki ma’aikatan lafiya sama da 15,000 aiki a karkashin shirin bunkasa sana’o’in da ake yi.

 

Dokta Salako ya ce ma’aikatar lafiya ta fara aiwatar da dokar kula da lafiyar kwakwalwa ta Najeriya, 2023, da nufin samar da cikakken sashen kula da lafiyar kwakwalwa a wani yunkuri na hada ayyukan kula da lafiyar kwakwalwa cikin harkokin kiwon lafiya na farko a fadin kasar nan.

 

Rediyon Najeriya da ke Sokoto ya rawaito cewa sabbin ayyukan da aka kaddamar sun hada da dakin gwaje-gwaje na Molecular, Sashen Kula da Lafiyar Jama’a, ICU, Cibiyar Kula da Dogaro da Magungunan Mata da Yara na Yanki, Cibiyar Ba da Agajin Gaggawa, Dakunan kwanan dalibai da yawa, Makarantar Koyon kula da masu tabin hankali, ICT da dai sauransu.

 

Shima da yake nasa jawabin, kwamishinan lafiya na jihar Sokoto, Dakta Faruku Wurno, ya nanata kudurin jihar na yin hadin gwiwa da asibitin ta Kware, inda ya bayyana yadda tsarin kula da lafiya na asibitin zai karfafa hadin gwiwa da bayar da hidima.

 

Dokta Wurno ya yabawa Daraktan kula da lafiya na asibitin Farfesa Shehu Sale bisa jajircewarsa da ya yi, ya kuma bukaci wadanda suka gaje shi da su kara azama kan taswirar ci gaban da aka riga aka shimfida.

 

NASIR MALALI

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kware Sakkwato kula da lafiyar kula da lafiya kiwon lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

 

Wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai da Hulda da Jama’a na Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, Folasade Boriowo, ya fitar, ta ce a karon farko cikin shekaru da dama, daliban Nijeriya za su ci gaba da karatun tarihin Nijeriya tun daga Firamare 1 zuwa karamar Sakandare 3 yayin da daliban SSS 1 – 3 za su koyi sabon darasin da aka samar na ‘Civic and Heritage Studies’, wanda ya hada tarihin Nijeriya da Ilimin zamantakewar Jama’a.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta