Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-02@21:12:50 GMT

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Ayukka 16 A Sakkwato

Published: 29th, May 2025 GMT

A wani babban ci gaba na kawo sauyi a tsarin kiwon lafiyar Najeriya, gwamnatin tarayya ta yi  ta kaddamar da ayyuka 16 a asibitin masu tabin hankali na gwamnatin tarayya dake Kware a jihar Sokoto.

 

Da yake jawabi a wajen bikin kaddamarwar, Ministan Kasa a ma’aikatar Lafiya da walwalar jama’a, Dokta Iziak Salako, ya jaddada cewa ayyukan na daga cikin ajandar sabuwar fata ta gwamnati shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu na karfafa cibiyoyin kiwon lafiya na kasa.

 

Ya ce FG ta himmatu wajen samar wa asibitoci kayayyakin more rayuwa, kayan aiki da kudade, da tallafi don inganta ayyukan hidima a fadin kasar.

 

Dakta Salako ya ci gaba da bayyana cewa, gwamnatin tarayya ta samar da muhimman ayyuka sama da 500 na samar da ababen more rayuwa tare da samar da ingantattun kayan aikin jinya ga manyan cibiyoyin kiwon lafiya a fadin kasar nan.

 

Ministan ya kuma bayyana cewa FG ta dauki ma’aikatan lafiya sama da 15,000 aiki a karkashin shirin bunkasa sana’o’in da ake yi.

 

Dokta Salako ya ce ma’aikatar lafiya ta fara aiwatar da dokar kula da lafiyar kwakwalwa ta Najeriya, 2023, da nufin samar da cikakken sashen kula da lafiyar kwakwalwa a wani yunkuri na hada ayyukan kula da lafiyar kwakwalwa cikin harkokin kiwon lafiya na farko a fadin kasar nan.

 

Rediyon Najeriya da ke Sokoto ya rawaito cewa sabbin ayyukan da aka kaddamar sun hada da dakin gwaje-gwaje na Molecular, Sashen Kula da Lafiyar Jama’a, ICU, Cibiyar Kula da Dogaro da Magungunan Mata da Yara na Yanki, Cibiyar Ba da Agajin Gaggawa, Dakunan kwanan dalibai da yawa, Makarantar Koyon kula da masu tabin hankali, ICT da dai sauransu.

 

Shima da yake nasa jawabin, kwamishinan lafiya na jihar Sokoto, Dakta Faruku Wurno, ya nanata kudurin jihar na yin hadin gwiwa da asibitin ta Kware, inda ya bayyana yadda tsarin kula da lafiya na asibitin zai karfafa hadin gwiwa da bayar da hidima.

 

Dokta Wurno ya yabawa Daraktan kula da lafiya na asibitin Farfesa Shehu Sale bisa jajircewarsa da ya yi, ya kuma bukaci wadanda suka gaje shi da su kara azama kan taswirar ci gaban da aka riga aka shimfida.

 

NASIR MALALI

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kware Sakkwato kula da lafiyar kula da lafiya kiwon lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Bug da kari Tinubu ya jinjina wa Shugaban jami’ar, Farfesa Wahab Olasupo Egbewole (SAN)da ‘yan tawagarsa wajen maida hankalin da suka yi na bunkasa Jami’ar da kumna kudurinta na muradun ci gaban da ake bukata.

Shi ma anashi jawabin Shugaban Jami’ar Sarkin Katsina, Alhaji. Abdulmumin Kabir Usman, wanda Wazirin Katsina, Sanata Ibrahim Idah ya wakilta, ya nuna jin dadinsa kan irin kokarin da UNILORIN saboda bunkasar ilimi da kumasamar wuraren koyon kaaratu masu kyau da kuma suka dace.

Ya yi ma kallon ayyukan da ak kaddamar a matsayin“ irin abubuwan da ake bukatar gani ke nan”da za su taimakawa lamarin koyarwa, koyo,da kuma bincike, inda ya kara da cewa yadda Jami’ar ta maida hankalinta wajen bunkasa dabarar koyon yin abubuwa zai taimakawa dalibai su tashi da sun koyi abubuwan da zasu yi baya rayuwar da suka yi cikin aji.

A nashi jawabin mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa. Egbewole ya nuna farin cikinsa da godew a Shugaban kasa Tinubu kan yadda ya amince da gaiyar da Jami’ar ta yi ma shi, da kuma taimaka mata wajen tafiyar da bunkasar abubuwan jin dadi.

“Muna nan muna sa ido saboda ci gaban samun abubwan da suke taimakawa ci gaba kwarai da gaske a kowace rana kamar yadda yace yana da amincewa da yardarm ci gaba da samun hakan’’.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna November 1, 2025 Manyan Labarai Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami November 1, 2025 Manyan Labarai Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida