Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Published: 31st, May 2025 GMT
“Ya zamar mana wajbi, mu kulla wannan hadakar, musamman domoin mu tabbatar da cewa, mun tsaftace tsarin,” Inji Dantsoho.
Ya kara da cewa, wannan aikin, ba wai kawai za kara habaka samar da kariya da kuma kara ingnata tsaro bane, har da kuma bayar da gagarumar gudunmawa, wajen kara ciyar da tattalin arzikin kasar nan gaba.
A cewar Shugaban, cunkoson da ake samu a Tashar ta Tin Can Island na ci gaba da haifar da jinkiri da rashin gudanar da ayyuka yadda suka kamata da kuma rage gudanar da hada-hadar kasuwanci, yadda ta kamata, wanda kuma hakan, ke janyowa kara habaka tattalin arzikin kasar.
Dantsoho wanda Babban Janar Manaja na sashen kula da tsaro a Hukumar ta NPA Mista Anthony Edosomwan ya wakilce shi a wajen kaddamar da aikin ya bayyana cewa, za a gudanar da aikin ne, zuwa kwana uku, musamman domin a samu nasarar gudanar da aikin.
Shugaban ya kara da cewa, sashen kula da tsaro na Hukumar ya wallafa a kafafen yada labarai, kan sanarwar wayar da kan jama’a kan batun mahimmancin, tsaftace Tashar ta Tin Can Island.
“Wannan wani mataki ne, da aka samu goyon bayan masu ruwa da tsaki ciki har da masu yin amfani da Tashar da ‘yan kasuwa da kuma sauran alummar da ke a kusa da yankin”, A cewar Dantsoho.
Shugaban ya ci gaba da cewa, Hukumar ta NPA ba za ta yi kasa a guiwa, wajen kara mayar da hankali da kuma zagewa, domin ta samu cin nasara wajen tabbatar da tsaftace muhalli da kuma samar da kyakyawan yanayi, a daukacin Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar ba.
“Yanayi na samun gurbatacciyar Iska da kutsen da ake yiwa Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar, abu ne da Hukumar ta NPA, ba za ta rungume hannu ta bari ba, ” Inji Dantsoho.
“Wannan aikin na tsafrace Tashar ba wai kawai na da alfanu ga ayyukan da ake gudanarwa a Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar bane, hatta alumomin da suke daura da Tashoshin, suma zai yi masu alfanu,“ A cewar Shuaban .
Shuaban ya kara da cewa, sashen kula da tsaro na Hukumar ta NPA da faro shi a wannan shekarar ta 2025, na daga cikin shiryae-shiryen rage cunkoso da kuma samar da saukin gudanar da ayyuka, Hukumar ta NPA, wanda hakan zai taimaka matuka wajen samar da kyakywar makoma ga Tashoshin Jiragen Ruwa, da ke a daukacin kasar nan.
A cewar Shugaban, wannan hadakar da sauran jami’an tsaro da kuma yin gangamin na wayar da kan alumma, Hukumar na bukatar goyon bayan alumma, dominn ta samu nasarar, aikin da ta sanya a gaba,
“A saboda haka, Mahukuntan Hukumar ta NPA, na bukatar goyon baya da hadin kan jama’a musamman domin a samar da kyakyawan yanin da ya dace a Tashar Jirgin Ruwan,” A cewar Shugaban.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Tashoshin Jiragen Hukumar ta NPA
এছাড়াও পড়ুন:
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
A wancan lokacin, sojojin Nijeriya sun musanta batun Shehun Borno, amma wasu na ganin cewa akwai kashan gaskiya dangane da wannan al’amari, sakamakon irin yadda ‘yan ta’addan ke cin karensu babu babbaka a wadannan yankuna.
Shi ma a nasa bangaren, mai sharhi kan kungiyoyin ta’addanci a Cibiyar Tony Blair, Barista Bulama Bukarti, ya ce, “A binciken da muke da shi, mun gano yadda Boko Haram suke amfani da jirage marasa matuka wajen kai wasu hare-hare a sansanonin sojojin Nijeriya.”
Idan an yi la’akari da wadannan bayanan sun nuna cewa kungiyar Boko Haram tana ci gaba da fadada ayyukanta a fannoni daban-daban ba tare da an taka mata birki ba.
Bisa ga wannan ne, Sanata Mohammad Ali Ndume, mai wakiltar kudancin Jihar Borno, ya ce dawowar hare-haren Boko Haram babban abin takaici ne wanda bai kamata gwamnati ta yi sakaci dangane da wadannan sabbin hare-haren da kungiyar take aiwatarwa a wasu yankunan jihar ba, musamman a sansanonin sojojin Nijeriya.
Duk da wasu shirye-shirye na dakile lamarin, Boko Haram ba ta daina aiwatar da munanan hare-hare kan sojoji da fararen hula ba. Saboda ko a cikin watan Maris na 2025, Boko Haram da ISWAP sun kai hari wani sansanin soja a Borno, inda suka kashe sojoji hudu tare da lalata makaman yaki, kamar yadda Kamfanin Reuters ya ruwaito. Sannan sun kai karin wani hari a sansanin rundunar hadin gwiwa ta MJTF da ke Wulgo, inda suka kashe sojoji 12 suka jikkata wasu goma sha biyu.
Abin bai tsaya nan ba, inda a ranar 12 ga watan Janairun da ya gabata, kungiyar ta kashe manoma 40 a Dumba kusa da Baga da ke Jihar Borno. Sannan kuma a ranar 12 ga watan Afrilun wannan shekara, a wani harin bam da kungiyar ta dasa a kan hanyar Maiduguri zuwa Damboa, ya kashe fararen hula takwas tare da jikkata karin wasu 21.
Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya bayyana fargabar cewa saura kiris karamar hukumar Marte, mai kimanin garuruwa 300 ya koma hannun ‘yan ta’adda, inda zancen da ake yi yanzu, gari daya ne kawai ya rage, wanda mayakan Boko Haram ba su mamaye ba, ya yi gargadin cewa bai kamata a bari ta fadawa a hannun ‘yan ta’adda ba.
Gwamnan ya yi wannan kan-da-garkin a ranar Lahadin da ta gabata, sa’ilin da ya kai wata ziyara a yankin, inda ya roki gwamnatin tarayya da ta yi amfani da dukkan matakan da suka dace cikin gaggawa wajen dakile yunkurin Boko Haram da ISWAP na kwace Marte.
A wannan ziyarar da Gwamna Zulum ya kai a Marte, domin gani da ido dangane da halin da ake ciki a yankin tare da kokarin lalabo mafitar zaman lafiya mai dorewa. A tattaunawarsa da manema labarai, gwamnan ya ce ziyarar ta zo ne don karfafa gwiwar al’ummar yankin, su samu juriya, da ci gaba da hadin kai tare da tallafa wa kokarin hukumomin tsaro.
Zulum ya kara da cewa, sakamakon matsalolin tsaro da yawan kai hare-hare ba kakkautawa a baya, hakan ya tilasta zakuda garin Marte; shekaru hudu da suka wuce, amma abin takaici, kwanaki uku da suka gabata, Boko Haram sun sake barnata gayin, al’amarin da ya jawo jama’a sake yin gudun hijira.
Ya ce, “Kimanin mutum 20,000 sun bar Marte zuwa Dikwa; wannan adadin babbar barazana ce, saboda zaman wannan adadi a sansanonin gudun hijira, akwai fargabar yawancin matasa su karkata zuwa shiga kungiyoyin ‘yan ta’adda.
“Wannan karamar hukumar Marte ta kunshi garuruwa da kauyuka sama da 300, amma yanzu gari daya kacal ya rage. Kuma muddin muka yi sakaci, ko shakka babu Marte zai fada hannun ‘yan ta’addan, wannan abin tsoro ne, kuma ina kyautata zaton hakan ba zai kasance ba.
“Saboda haka, ina kira ga gwamnatin tarayya tare da sojojin Nijeriya, mu hada kai wajen hana yuwuwar faduwar Marte zuwa ga kungiyar Boko Haram,” In ji Zulum.
Zulum ya nuna karfin gwiwarsa da cewa, mafi yawan ‘yan gudun hijira sun fara komawa bayan wannan ziyarar da ya kai tare da yaba da kokarin hukumomin tsaro da masu aikin sa-kai.
“Alhamdulillah, mun shiga garin Marte jiya kuma mun kwana tare da taimakon sojojin Nijeriya da masu aikin sa-kai, kuma al’umma sun zauna karo na biyu. Duk da haka, addu’ar da nake yi, Allah ya sa gwamnatin tarayya da sojojin Nijeriya su yi duk abin da za su iya don kiyaye wannan garin,” in ji shi.
Har ila yau kuma, gwamnan ya sake jaddada aniyarsa na tallafa wa sojojin Nijeriya a kokarinsu na dawo da zaman lafiya a fadin Jihar Borno.
Gwamna Zulum, ya yi zargin cewa wasu ‘yan siyasa da jami’an sojojin Nijeriya suna da hannu wajen rura wutar matsalolin tsaro, ta hanyar bai wa ‘yan ta’adda bayanan sirri tare da hadin gwiwa da ‘yan ta’addan Boko Haram.
“Wadannan ‘yan ta’adda suna da masu ba su bayanan sirri tare da hadin gwiwa a cikin sojojin Nijeriya, da kuma cikin ‘yan siyasa, da kuma cikin al’umma. Saboda haka, babban abin da za mu yi shi ne, dole mu karfafa hanyoyin samar da bayanan sirri na leken asiri don dakile wadannan matsaloli.”
Gwamnan ya sake jaddada cewa akwai bukatar Nijeriya ta samar da sabbin dabarun yaki da ta’addanci domin samun dawamamen zaman lafiya, tare da dakile hanyoyin ta’addanci.
A wani rahoton da BBC Hausa ta fitar, baya ga karamar hukumar Marte, akwai karin wasu kananan hukumomi wadanda suke fuskantar barazanar Boko Haram a Jihar Borno, wadanda suka hada da Bama, wanda a tattaunawar, Dakta Kabir ya bayyana Bama a matsayin wuri mafi tsanani samun hare-haren Boko Haram suka tagayyara a jihar.
Sauran sun hada da karamar hukumar Konduga, gari ne wanda yana daya daga cikin wuraren da hare-haren Boko Haram suka yi kamari. Sai Gwoza, Dikwa, Askira-Uba, Damboa, Mafa da Jere duk a Jihar Borno.
Wasu rahotanni sun bayyana cewa kimanin manoma 50 ne ake zargin mayakan Boko Haram sun kashe ta hanyar yi musu yankan rago, a kauyen Malam Karanti, da ke karamar hukumar Kukawa a Jihar Borno.
Wadannan manoman sun kasance a karkashin kulawar daya daga cikin kwamandojin kungiyar ISWAP, wanda ake kira Amir Akilu, wanda aka ce shi ne yake kula da kauyukan Malam Karanti zuwa Dawashi, wanda suke bai wa manoma da masunta tsaro, su kuma suna biyan haraji akai-akai ga kungiyar ‘yan ta’addan.
Wata majiyar ta bayyana cewa kungiyar ISWAP sun kai harin ne sakamakon zargin manoman da yi musu leken asiri zuwa ga jami’an tsaro.
Daya daga cikin wadanda suka tsallake rijiya da baya a harin, ya ce ‘yan ta’addan sun kewaye manoman tare da yi musu barazanar kasa duk wanda ya yi kokarin gudu.
“Wasu daga cikinmu sun fara roron wake sa’ilin da suka kai mana wannan hari. Sannan kuma suka tattara mu, suka bayyana mana cewa za su harbe duk wanda ya yi kokarin gudu. Sun yanka mutane da yawa, na ga wadanda aka yi wa yankan rago da idona. Amma na zabi na gudu maimakon in jira a yanka ni.
“Sun kashe fiye da mutum 50, kuma mafi yawa an yi musu yankan rago. Haka kuma sun sace wasu” in ji shi.
Haka kuma Gwamna Zulum ya yi zargin cewa, sojojin Nijeriya ba su da isassun kayan aikin da suke bukata wajen tunkarar ‘yan ta’addan Boko Haram.
Gwamnan ya bayyana hakan a wata hira da ya gudanar da manema labarai, ya ce ‘yan ta’addan a halin yanzu suna amfani da fasahar zamani wajen aiwatar da hare-haren ta’addanci.
Zulum ya bukaci Shugaba kasa Bola Tinubu ya saurari sojoji kan abubuwan da suke bukata don kawo karshen ta’addanci a arewacin kasar nan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp